Tawagar motocin Babban Kwamandan Runduna (GOC) ta 8 kuma Kwamandan Sashi na 2 na Rundunar Haɗin Gwiwa ta North-west Operation Fansan Yamma, Manjo Janar Bemgha Koughna, ta daƙile wani kwanton ɓauna da ake zargin ’yan ta’addan Lakurawa ne suka shirya a kusa da Tudun Mayama a Jihar Kebbi.
Harin ya faru ne yayin da tawagar GOC ɗin take kan hanyar ta ta zuwa duba dakarun da ke kan gaba a jihar.
A wata sanarwar manema labarai da Muƙaddashin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji ta 8, Rundunar Sojin Nijeriya / Sashi na 2 na Operation Fansan Yamma, Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, ya fitar a yau Litinin, ya bayyana cewa tawagar ta fuskanci harbi mai tsanani ba zato ba tsammani daga ’yan ta’adda masu ɗauke da makamai yayin da suke wucewa ta cikin dazuzzukan yankin da ke da haɗari.
Ya ce: “Da nuna ƙwarewa ta musamman wajen jagoranci da dabarun yaƙi, Manjo Janar Koughna da dakarun sa sun mayar da martani da ƙarfi, inda suka hallaka ’yan ta’adda biyar tare da fatattakar kwanton ɓaunar.
“Wannan aiki ba kawai ya kare tawagar ba ne, har ma ya tarwatsa shirye-shiryen ’yan ta’addan, tare da isar da saƙo mai ƙarfi na tsoratarwa ga ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya da suka daɗe suna addabar al’ummomin yankin.
“Bayan nasarar da aka samu, dakarun sun gudanar da cikakken bincike a yankin, inda suka ƙwato tarin makamai da kayayyakin bayanan sirri masu yawa.”
Ya ƙara da cewa kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindiga samfurin OJC guda ɗaya, bindiga PKT guda ɗaya, bindigogi AK-47 guda biyu da kuma kwandunan harsasai na AK-47 guda huɗu.
Sauran sun haɗa da laya (bandolier) guda ɗaya ta harsasan PKT, harsasai da dama na 12.7mm, jakar raƙumi mai ɗauke da kuɗi Naira 840,000, wayoyin hannu guda biyu da babura guda biyar.
Osoba ya ce: “A halin yanzu, dakarun na nan a yankin cikin shiri da taka-tsantsan, suna tabbatar da cikakken iko domin hana sake faruwar hare-hare.
“Wannan aiki ya nuna jajircewar Runduna ta 8 ta Sojin Nijeriya wajen kare fararen hula da kuma kawar da barazanar ta’addanci a yankin Arewa-maso-yamma.”







