• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa

Fati Abdul by Fati Abdul
May 8, 2026
in Tsaro
A A
0
’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa
'Yan sanda sun shanya waɗanda ake zargi da aikata laifin garkuwa da mutane a Rukubi

'Yan sanda sun shanya waɗanda ake zargi da aikata laifin garkuwa da mutane a Rukubi

’Yan sanda sun kama mutane takwas da ake zargi da aikata garkuwa da mutane bayan wani samame na tsaro na haɗin gwiwa da aka gudanar a ƙauyen Rukubi da ke Ƙaramar Hukumar Doma a Jihar Nasarawa.

Jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya a Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, DCP Anthony Okon Placid, ya bayyana a cikin wata sanarwar manema labarai a wannan Juma’a cewa an gudanar da aikin ne bayan samun rahoton gaggawa a safiyar yau, 7 ga Mayu, 2026, dangane da wani hari da wasu ’yan bindiga suka kai bayan sun mamaye ƙauyen a daren jiya, suna ta harbe-harbe barkatai tare da haddasa firgici a tsakanin mazauna yankin.

Ya ce: “A yayin harin, an ruwaito cewa maharan sun kutsa cikin gidajen wasu mazauna biyu tare da yin garkuwa da mutum biyu zuwa wani wuri da ba a sani ba.

“Bayan samun rahoton, jami’an ’yan sanda na Rundunar Jihar Nasarawa, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro da matasan al’umma na yankin, sun gaggauta isa wurin tare da ƙaddamar da samamen haɗin gwiwa wanda ya kai ga kama mutum takwas da aka alaƙanta da lamarin.”

Makamai da ‘yan sanda suka ce sun karɓa a hannun waɗanda ake zargi

Waɗanda aka kama sun haɗa da Adamu Alfa, Muhammed Alfa, Shu’aibu Alfa, Usman Alfa, Ali Alfa, Isa Alfa, Adamu Alfa, da Ja’afaru Alfa, dukkan su daga Rugan Alhaji Alfa da ke ƙauyen Rukubi.

Mai magana da yawun ‘yan sandan ya ƙara da cewa a yayin aikin, jami’an tsaro sun ƙwato bindigogi biyu ƙirar AK-47, babura huɗu ƙirar Bajaj, da kwanson harsasai biyu na 7.62mm da aka harba, waɗanda ake zargi da harin.

A cewar sa, ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin ya samu munanan raunuka a yayin artabun, kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwar sa yayin da yake karɓar magani.

Ya ce: “Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, IGP Olatunji Rilwan Disu, psc(+), NPM, ya yaba da jarumtaka da ƙwarewar jami’an da suka gudanar da aikin, yana mai bayyana nasarar a matsayin wata babbar shaida ta ingancin aikin ’yan sanda da ke amfani da bayanan sirri da kuma haɗin gwiwar hukumomi wajen yaƙi da manyan laifuffuka masu tada hankali.

“Haka kuma ya yaba da gagarumar gudunmawar hukumomin tsaro na abokan aiki, ƙungiyoyin sa-kai na tsaro, matasan al’umma, da mazauna yankin, waɗanda haɗin kan su ya taimaka matuƙa wajen samun wannan nasara.”

Tags: 'yan sandaAnthony Okon PlacidDomakidnappersNasarawapoliceRukubisuspectsɓarayi
Previous Post

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

Next Post

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya
Tsaro

‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya

April 16, 2026
Next Post
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!