• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Mahanga

Yadda Aka Raba Musulmi Da Ƙur’ani

ALI ABUBAKAR SADIQ by ALI ABUBAKAR SADIQ
February 22, 2026
in Mahanga
A A
0

 

Babbar annobar da ta hana Musulmi zama lafiya da juna da samun koma-baya a al’amurra tsawon kimanin shekaru 1,300 shi ne raba su da Ƙur’ani da aka yi cikin hikima. Wasu za su yi wuf su ce ta yaya za a ce an raba Musulmi da Ƙur’ani bayan a gidan kowanne Musulmi akwai Ƙur’ani, sannan aƙalla sau biyar a rana suna karanta shi, baya ga tilawa a kai a kai ko jefi-jefi da kusan kowanne Musulmi ke yi, tare da bajekolin tafsirin sa sau guda a shekara cikin watan azumi, sannan a kullum yara na hadda da tilawa baya ga musabaƙa?

Haƙiƙa, duk waɗannan abubuwa da na jero haka suke, wataƙila ma da waɗanda ban saka ba. To ta yaya aka raba Musulmi da Ƙur’anin? Cikin Suratul Furƙan Allah ya ba mu labarin cewa a ranar lahira:

“Kuma Manzo ya ce: ”Ya Ubangijĩ na! Lalle mutãne na (Musulmi) sun riƙi wannan Alƙur’ãni abin ƙauracẽwa!” (Ƙ25:30)

Daga bakin da ba ya ƙarya, a ranar lahira Annabi zai kai ƙorafin mu wajen Ubangiji cewa “mun ƙaurace wa” Ƙur’ani. Kalmar da Allah ya yi amfani da ita, ita ce “Mahjura” daga “Hijr” wato yayi da ka bar wani abin ka ka musanya da wani. Wannan ita ce cikakkiyar hujja ta farko cewa mun rabu da Ƙur’ani duk da waɗancan dalilai na sama da muka kawo, kuma ƙorafin Annabi na farko ga Ubangiji shi ne: ya kawo mana Ƙur’ani, mun karɓa hannu biyu-biyu amma mun ƙaurace masa daga baya. Aya mai bin wannan, wato ta 29, ga abin da ta ke cewa:

“‘Lalle ne, haƙĩƙa ya ɓatar da ni daga Tunãwa (Ƙur’ani) a bãyan (Tunãwar) ta je mini. Kuma Shaiɗan ya zama mai zumɓulẽwa ga mutum.” (Ƙ25:29)

A wannan aya kuma Allah ya yi amfani da kalmar “Zikri” (wani suna da Allah ke kiran Ƙur’ani da shi), yadda a bayan wancan caji da Annabi zai mana a gaban Ubangiji ranar Lahira, cikin mu wanda duk ya ƙaurace wa Ƙur’ani, amsar da zai bayar kenan ta nadamar cewa duk da Allah ya bamu Ƙur’ani amma mun yi watsi da shi.

Masaniyar haɗarin da ƙaurace wa Ƙur’ani zai jefa al’ummar sa, shi ya sa tun yana raye Annabi ya hango hanya mai haɗari da za ta assasa haka, inda cikin wani hadisi ya zo cewa:

“An ruwaito daga Abu Sa’eed al-Khudri cewa Manzon Allah (Mai tsira da aminci) ya ce: “Kada ku rubuta wani abu daga gare ni; duk wanda ya rubuta wani abu daga gare ni ba Ƙur’ani ba, ya goge shi.” (Muslim ne ya ruwaito hadisi na 5,326)

Har Annabi yayi wafati, Khulafa’u Rashidun suka kauce, wannan gargaɗi na Annabi ya yi tasiri domin ya shiga kunnuwan sahabban sa, yadda babu wani cikin su da ya zauna ya rubuta hadisan Manzon Allah. Dalilin haka ya sa ɗaukacin su suka rayu a tarbiyyar bin Ƙur’ani sau da ƙafa.

Abu na farko da ya kutso kai wájen kassara Ƙur’ani shi ne maganar Nasikh wal Mansukh, wato wata aya ta shafe wata a cikin Ƙur’ani.

Wannan mas’ala ba a taɓa karo da ita zamanin Annabi na raye ba, sai bayan wafatin sa inda Tabi’ai suka fara yi wa Sahabbai tambaya a kan ko wata aya ta soke wata. Wataƙila kasancewar mutanen da ba su rayu da shi ba suna ganin kamar wata aya ta ci karo da wata, kuma ƙarancin ilimi ya sa aka dinga ɗaukar hakan. Amma babu wata aya da ta yi karo da wata a Ƙur’ani (ina da cikakken rubutu kan wannan maudu’in mai taken, “Waɗanne Ayoyi Aka Soke a Ƙur’ani?”).

Ta yaya Ubangijin da ya san komai, ya rubuta littafin nan a lauhul mahfuz, sannan zai zo cikin shekaru 23 kacal, ya riƙa kwan-gaba-kwan-baya na soke-soke? Hatta kundin tsarin mulkin Amurka sai da ya yi shekaru sama da ɗari kafin a fara gyara shi, ballantana kundin tsarin mulkin Allah.

Kuma abin sha’awa shi ne a farkon ƙarni na 10 bayan wafatin Manzo, an ce akwai kimanin ayoyi 564 da ake cewa wata ta soke wata, amma sannu a hankali ana ta rage adadin, domin a ƙarni na 11 sai Hibbatullah ya ce akwai ayoyi 237.

Haka dai, haka dai har zuwa ƙarni na 17 inda Suyuɗi ya ce saura ayoyi 20, yayin da a ƙarni na 20 kuma Shah Waliyyullah ya ce saura 5 kacal. A rubutu na, na ɗauko duk biyar ɗin na nuna hujjar cewa babu wadda ta yi karo da ‘yar’uwar ta, kowacce na aikin ta har gobe.

Don haka a bayyane yake sakamakon yadda aka yi ta zabtare adadin daga sama da 500 zuwa 5, ya nuna cewa ƙarancin fahimta ya kawo zaton karo da juna.

Shigo da soke ayoyin Ƙur’ani naƙasu ne da ake jingina wa Ƙur’ani da mawallafin sa, kuma ya ba da damar laluben hadisai domin gamsar da bambanci. Sannu a hankali sai malamai irin su Malik suka bayyana, domin shi ne ya fara assasa rubutun hadisi da dogaro a kan sa fiye da Kur’anin – abin da Annabi ya ji mana tsoro.

Daga nan kuma sai aka shigo da maganar fiƙihu wanda ya daɗa bai wa hadisai tasiri fiye da Ƙur’ani. Aƙidu na ƙungiyanci suka samu gindin zama kamar yadda fitina tsakanin Musulmi ita ma ta share wuri ta zauna yadda har yanzu take maguza mu.

Amma da halifofin Abbasidawa suka karɓe mulki daga Umayyadawa a 750 AD, kuma suka rungumi koyarwar Ƙur’ani, sai ga shi Musulunci ya samu haɓaka, musamman a fannonin ilimi, yadda aka kafa harsashin kimiyya da ta zama cibiyar kimiyyar zamani da muke mora a yau.

Haka nan Daular Andalusiya da ta ɗauki biyayya ga Ƙur’ani sai ga shi ta yi fice a duniya yadda babu mai cigaban ta a zamanin ta.

Amma da malamai irin su Ahmad Bin Hanbal da su Ghazali suka samu gaba sai aka hura usur ɗin komawa ga salaf da riƙo da hadisi fiye da Ƙur’ani.

Idan ka duba tarihin mazhabobi, zai bayyana gare ka cewa mafi tsufan mazhaba ta Hanafi (699-767AD) ba ta kai mai bin ta, wato Malikiyya (711–795AD) amfani da hadisi ba. Haka nan mazhabar Shafi’i (767–820 AD) sai ta zo ta daɗa kambama aiki da hadisi fiye da ta Malik. Domin Shafi’i ya kai ga daidaita ƙarfin hadisi tamkar Ƙur’ani.

Za mu tuna shahararriyar maganar sa a masallacin Annabi cewa: “Ana iya watsi da maganar kowa, har tawa, ban da wanda ke kwance a nan” – ya nuna kabarin Annabi.

Shafi’i ya yi shura wajen fifita hadisi kan Ƙur’ani cikin mazhabar sa, kuma ya samu ƙalubale daga wasu Malikawa, musamman Yatsar wanda a sakamakon muƙabala da shi ya janyo yaran Yatsar suka lakaɗa masa duka, abin da ya yi sanadiyyar ajalin sa.

To amma uwa-uba, mazhabar Hanbali (780 – 855 AD) ta yi musu fintinkau wajen dogaro da hadisai. Domin saɓanin Abu Hanifa, wanda kashi ƙasa da goma ya ba da karfi ga hadisi, shi Ɗan Hanbal kashi 95% ya bai wa hadisai.

Amfani da hadisi ba illa ba ne ko kaɗan, inda illar ta ke shi ne fifita shi da aka yi kan Ƙur’ani. Da a ce malaman mazhabobi sun tafi a irin tsarin Abu Hanifa, da wataƙila ba mu samu kan mu cikin ruɗanin da muke ciki ba. Imam Abu Hanifa, cikin littafin sa Al alim wal Muta’allim,  shafi na 175, ya ce:

“Idan wasu mutane suka zo mana da hadisi wanda ba mu san shi ba, kuma ba za mu iya daidaita shi da sanin mu ba a hankalce, sai mu koma ga Allah, mu aje hadisin.”

Sannan Abu Hanifa ya sake cewa:

“Na yi imani da duk abin da Annabi ya faɗa. Amma shi Annabi ba zai taɓa faɗar wani abu na zalunci ba ko wanda ya saɓa wa Ƙur’ani. Saboda faɗar Allah cewa:

“Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu. Dã Mun kãma shi sannan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã. Kuma daga cikin ku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbar Mu) daga gare shi.” (Ƙ69:44)

Wannan ita ce ingantacciyar tarbiyyar da aka watsar, wato ɗora hadisi a kan sikelin Ƙur’ani, ilimi da hankali. Wannan aya ta tabbatar mana kamar yadda Abu Hanifa ya ce, babu ta yadda za a ce Annabi zai saba wa ayar Ƙur’ani da sunnar sa (Hadisi).

Kamar yadda na faɗa a farkon rubutun, a zahiri kamar muna riƙe da Ƙur’ani amma idan ka kalli rayuwar mu sai ka ga ta yi hannun riga da koyarwar Ƙur’ani. Hukunce-hukunce ƙarara na Ƙur’ani an yi watsi da su an lalubo na hadisi an maye gurbin su da su. Domin akasarin matsalolin da ake tataɓurza tsakanin Musulmi tun wancan lokaci zuwa yanzu, za ka samu suna da cikakken bayani a Ƙur’ani, amma kwata-kwata ba a amfani da su sai waɗanda aka ƙirƙira, domin babu yadda Annabi, kamar yadda Abu Hanifa ya faɗa, a koyarwar sa ta hadisi ya saɓa da Ƙur’ani.

Shi ya sa manyan matsaloli da ake tada jijiyar wuya a Musulunci za ka samu watsi da koyarwar Ƙur’ani tare da ɗaukar ƙirƙirarru daga hadisi ya janyo su, misali:

1. Hukuncin jefe mazinaci
2. Iyayen Annabi a wuta
3. Hukuncin ɗan shege
4. Matsayin ahlul Kitab
5. Sakin Aure
6. Ɓatanci ga Annabi
7. Ridda
8. Kafirta Musulmi
9. Abinci da ya haramta
10. Lokacin fitar da zakka, da.

Bayan mai da Ƙur’ani gidan baya an turo hadisi gaba, abu na gaba da aka yi wajen raba Musulmi da Ƙur’ani shi ne saka a riƙa yi masa karatun aku, wato ƙira’a ba tare da fahimtar me kake karantawa ba, tamkar yadda idan ka yi zagi, aku zai maimaita ba tare da sanin abin da ya faɗa ba. Rararara, muna karanta shi kullum cikin sallolin mu amma ba mu san me muke faɗa ba, saboda an gina al’adar cewa ba za ka fahimci tarjamar sa ba sai ka san lugga da nahawun Larabci, ka san sira da fiƙhu, wato an kwaikwayi ruhubaniyanci kenan yadda ba mai isa ga Allah sai wanda yi bi ta hannun fasto kenan ko?

Haƙiƙa, akwai sassa na Ƙur’ani da dole sai ka san fannoni za ka iya zaƙulo ma’ana ta wasu ayoyi, amma waɗannan ayoyi ƙalilan ne, kamar yadda Allah ya ce:

“Shi ne wanda ya saukar da Littãfi a gare ka, daga cikin sa akwai ãyõyi bayyanannu, su ne mafi yawan Littãfin, da wasu mãsu kamã da jũna.” (Ƙ3:7)

Ba ka buƙatar kowanne irin ilimi domin ka gane ayoyi irin su “Allah ɗaya ne bai haifa ba, ba a haife shi ba,” “Kada ku kusanci zina,” ‘Kada ku ce wa iyaye uffan,” “Ku cika alƙawari,” “ban da sata,” ko “shaidar zur” da yawancin ayoyin waɗanda su ne mafi yawan littafin kamar yadda ayar ta ce. Shi ya sa ma Allah ya ƙalubalance mu da cewa:

“Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur’ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?” (Ƙ54:17)

Sannan a baya-bayan nan sai wata ƙungiya ta bayyana a fusace, kamar yadda Wahabiyanci ya zo a fusace, wato ‘yan Ƙur’aniyyun, da cewar a watsar da duk wani hadisi a yi aiki da Ƙur’ani kawai.

Shi tsanani daga duk siffar da ya fito za ka samu yana da illa fiye da maganin da ya zo yi. Don haka sai wannan tsari ya daɗa nesanta mutane da Ƙur’ani, yadda wasu ke kallon wanda ya ce Ƙur’ani zallá kawai, kamar kafiri ne. Muna gani yadda a yanzu wasu malamai a ƙoƙarin nuna gazawar Sheikh Masussuka, sai su ɓige da nuna gazawar Ƙur’ani.

Wajibi ne a fifita Ƙur’ani sama da komai, amma kuma matuƙar za ka yi aiki da shi dole ka tafi da sauran ilimai, domin abin da Ƙur’ani ya tabbatar shi ne:

“…Kuma akwai daga mutãne wanda ke yin jidãli ga al´amarin Allah, bã da wani ILIMI ba, kuma bã da wata SHIRIYA ba, kumã ba da wani LITTAFI mai haskakãwa ba.” (Ƙ31:20)

Wato abubuwa uku Allah ya aminta da su waɗanda mutum zai iya dogaro da su wajen kafa hujja da su:

1. ILIMI, duk wani Ilimi ingantacce na al’ada, tarihi ko wata masaniya da aka tabbatar, ds.

2. SHIRIYA walau hadisi ingantacce, kimiyya, falsafa da sauran su. Duk wani ilimi mai amfani hikima ce da Allah ya saukar wa bayin sa, kamar yadda ya jaddada:

 “Yana bãyar da hikima (ga fahimtar gaskiyar abubuwa) ga wanda Yake so. Kuma wanda aka bai wa hikima to lalle ne an bã shi alhẽri mai yawa. Kuma bãbu mai tunãni fãce ma’abuta hankula.” (Ƙ2:269)

3. LITTAFI wanda ya kewaye duk saukakkun littattafai (kamar yadda malaman fassara irin su Ibn Kathir, Tabari da sauran su suka riƙa amfani da israiliyyat cikin tafsiran su).

Amma dai mu sani cewa madogarar farko da ta ƙarshe ita ce Ƙur’ani, kuma abin da muka yi watsi da shi kenan a yau. Dole mu gane cewa wallahi Musulmi mafitar mu ɗaya ce, kamar yadda Allah ya tabbatar mana cewa:

“Shin, lõkaci bai yi ba ga waɗanda suka yi ĩmãnĩ (Musulmi) zukãtan su su yi tawali’u ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya (Ƙur’ani)? Kada su kasance kamar waɗanda aka bai wa littãfi a gabãnin haka, sai zãmani ya yi tsawo a kan su, sabõda haka zukãtan su suka ƙeƙashe, kuma masu yawa daga cikin su fãsiƙai ne.” (Ƙ57:16)

Wannan aya kai-tsaye da mu take ba da sahabbai ba, domin su sun rayu a kan Ƙur’ani. Shin lokaci bai yi ba da za mu koma kan sa? Ɗaruruwan shekaru an mai da Ƙur’ani baya, Allah yana mana gargaɗi kada mu zama irin Yahudu da Nasara waɗanda suka yi watsi da koyarwar littafin su bayan tsawon lokaci. Riƙo da Ƙur’ani shi ne matakin tsira, sannan hadisi ko wani ilimi ya biyo baya.

Matuƙar Ƙur’ani zai zamar mana ma’auni, kuma mu dabbaƙa shi cikin rayuwar mu, to wallahi da sai mun magance kowace irin matsala. Ya rage namu, mu yi riƙo da shi ko mu ci gaba da ƙaurace masa, mu sani dai duk wanda ya ƙaurace wa Ƙur’ani za su raba gari da Manzo a ranar lahira domin su ne waɗanda Manzo zai kai ƙara a wajen Allah cewa:

“Kuma Manzo ya ce: ‘Ya Ubangijĩ na! Lalle mutãne na (Musulmi) sun riƙi wannan Alƙur’ãni abin ƙauracẽwa!”‘ (Ƙ25:30)

Allah ya sa mu dace.

Tags: AllahAnnabi SAWhadisaiƘur'ani
Previous Post

Tinubu ya taya APC murnar nasara a zaɓuɓɓukan Birnin Tarayya, Kano da Ribas

Next Post

Tawagar motocin kwamandan rundunar soji ta daƙile mummunan kwanton ɓauna a Kebbi, ta hallaka ’yan ta’adda 5, ta ƙwace tarin makamai

Related Posts

Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?
Mahanga

Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?

March 29, 2026
Taƙaddamar Imam Ghazali Da Ibn Rushud A Kan Ruhi (Rai)
Mahanga

Taƙaddamar Imam Ghazali Da Ibn Rushud A Kan Ruhi (Rai)

February 18, 2026
Musulunci Da Masu Yi Masa Zagon Ƙasa A Nijeriya
Mahanga

Musulunci Da Masu Yi Masa Zagon Ƙasa A Nijeriya

February 15, 2026
Sarkin Adabi: Mafi Girman Sarautar Fasaha
Mahanga

Sarkin Adabi: Mafi Girman Sarautar Fasaha

February 13, 2026
Muhimman Shawarwarin Tsaro Ga Magidanta Da Iyalai
Mahanga

Muhimman Shawarwarin Tsaro Ga Magidanta Da Iyalai

January 20, 2026
Tinubu ya sha alwashin ganin bayan maƙiyan Nijeriya, ya girmama marigayi Abubakar Audu
Mahanga

Muhimmin lokaci a Nijeriya: Hujjar da ta sa hanyar da aka ɗauka ita ce mai ɓullewa

January 4, 2026
Next Post
Tawagar motocin kwamandan rundunar soji ta daƙile mummunan kwanton ɓauna a Kebbi, ta hallaka ’yan ta’adda 5, ta ƙwace tarin makamai

Tawagar motocin kwamandan rundunar soji ta daƙile mummunan kwanton ɓauna a Kebbi, ta hallaka ’yan ta’adda 5, ta ƙwace tarin makamai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!