• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Friday, May 15, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

Wakilin Mu by Wakilin Mu
May 9, 2026
in Tsaro
A A
0
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu, tare da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, lokacin da ya kai ziyarar aiki ta kwana uku a Amurka

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu, tare da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, lokacin da ya kai ziyarar aiki ta kwana uku a Amurka

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu, tare da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, lokacin da ya kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Amurka

Nijeriya da Amurka sun ƙulla yarjejeniyar ƙara zurfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, yaki da ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin Yammacin Afrika.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Shugaban Kasa kan Yada Labarai, Bayo Onanuga, ya fitar a yau Asabar.

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu, ya kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Amurka, inda ya gana da manyan ƙusoshin gwamnatin ƙasar.

A yayin ziyarar, Ribaɗu ya isar da saƙon Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jajircewa wajen ɗorewar dangantakar da ke tsakanin ƙasashen biyu.

Ribaɗu ya gana da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, da sauran manyan jami’an diflomasiyya da na tsaro na Amurka.

Babban maƙasudin wannan ganawa shi ne duba yadda za a inganta raba bayanan sirri da kuma ƙarfafa ayyukan soji na haɗin gwiwa.

Ribaɗu ya jaddada muhimmancin taimakon juna don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Sahel, musamman Ayyukan ta’addanci da tsageranci, safarar miyagun ƙwayoyi da makamai da laifukan da ake aikatawa ta hanyar yanar gizo.

Hukumomin Amurka sun jinjina wa Nijeriya a matsayin ta na jagora a yankin Afrika, musamman wajen jagorantar yaƙi da ta’addanci a tafkin Chadi.

A nata ɓangaren, Nijeriya ta bayyana cewa tana amfani da dabarun ƙarfin soja da kuma tattaunawa da inganta rayuwar jama’a don magance tushen matsalar rashin tsaro.

“Nijeriya tana godiya ga Amurka bisa taimakon da take bayarwa a ɓangaren horar da jami’ai, ba da bayanan sirri, da kuma tallafin jinkai,” inji Ribaɗu.

A ƙarshen taron, ɓangarorin biyu sun amince su ci gaba da tuntuɓar juna a kai a kai ta hanyar haɗin gwiwa na musamman don tabbatar da cewa dukkan yarjejeniyoyin da aka ƙulla sun fara aiki yadda ya kamata.

Tags: JD VanceNuhu Ribadutsaroyarjejeniya
Previous Post

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

Next Post

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa
Tsaro

’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa

May 8, 2026
Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya
Tsaro

‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya

April 16, 2026
Next Post
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!