Hedikwatar Tsaro (DHQ) ta bayyana cewa dakarun ƙasar nan sun samu nasarar ragargazar ɗimbin ’yan ta’adda, inda suka kama wasu da dama tare da ceto mutum sama da 50 da aka yi garkuwa da su a faɗin ƙasar.
Waɗannan nasarori sun faru ne a yayin ayyukan kakkaɓa da sojoji suka gudanar tsakanin ranar 30 ga Afrilu zuwa 7 ga Mayu 2026.
Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja.
Ga yadda nasarorin suke kasance a kowace shiyya:
• Arewa maso Gabas (Operation HADIN KAI): Rundunar ta dakile hare-haren ’yan ta’adda a Magumeri da ke Jihar Borno. Haka kuma, wasu daga cikin maharan sun mika wuya, yayin da aka kama masu kai musu kayan abinci da makamai.
• Arewa maso Yamma (Operation FANSAN YAMMA): Sojoji sun yi artabu da ’yan fashi a jihohin Katsina da Zamfara, inda aka kashe da dama tare da ƙwace babura da makamai.
• Arewa ta Tsakiya (Operation SAVANNAH SHIELD): An ceto waɗanda aka yi garkuwa da su tare da kama masu safarar harsasai har guda 250 a cikin birnin Abuja.
• Jihar Filato: Jami’an tsaro sun bankaɗo wata maƙerar makamai ba bisa ƙa’ida ba a Jos ta Kudu, inda aka kama mutanen da ake zargi da ƙera bindigogi.
• Jihar Binuwai da Kogi: An samu nasarar ceto wasu yara ɗalibai da aka sace daga gidan marayu.
Janar Onoja ya ƙara da cewa, dakarun Operation DELTA SAFE a Kudancin ƙasar nan da kuma Operation UDO KA a Kudu maso Gabas duk sun samu nasarar kama masu garkuwa da mutane da kuma dillalan makamai na kungiyar IPOB/ESN.
Ya ce: “Rundunar sojin ƙasa a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Hafsun Tsaro, Olufemi Oluyede, ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa ’yan Nijeriya sun rayu cikin lumana da kwanciyar hankali.”
Wannan gagarumar nasarar ta nuna cewa jami’an tsaro sun sake zage damtse wajen ganin sun kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka addabi sassan ƙasar nan.







