Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya kai ƙarar hukumar ICPC, Babban Alƙalin Majistare na FCT, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda da Babban Lauyan Tarayya a Babbar Kotun Tarayya saboda binciken da jami’an ICPC suka gudanar a gidan sa ranar 19 ga Fabrairu, 2026.
A ƙarar, ya roƙi kotun da ta ayyana takardar izinin binciken a matsayin mara inganci.
Shari’ar, wadda ke neman a tabbatar da kare haƙƙoƙin sa na asali, ta ambaci ICPC, Babban Alƙalin Majistare na FCT, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda da Babban Lauyan Tarayya a matsayin waɗanda ake ƙara.
Mai Ba shi Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Muyiwa Adekeye, ya faɗa a wata takardar manema labarai a yau Litinin cewa shari’ar na neman kotu ta ayyana cewa:
• Takardar izinin binciken ba ta da inganci saboda rashin takamaiman bayani, kurakurai na rubutu masu muhimmanci, rashin bayyana sharuɗɗan aiwatarwa yadda ya kamata, wuce gona da iri da kuma rashin hujjar zargi mai tushe.
• Kutse da binciken gidan sa bisa takardar izini mara inganci babban take ne ga haƙƙoƙin sa na ɗan’adam da suka haɗa da mutuncin ɗan’adam, ‘yancin kai na mutum, sauraron shari’a cikin adalci da kuma sirri, kamar yadda Sashe na 34, 35, 36 da 37 na Kundin Tsarin Mulki suka tanada.
• Duk wata shaida da aka samu bisa wannan takardar izini mara inganci da bincike ba bisa ƙa’ida ba ba za a amince da ita ba a kowace shari’a da ake yi a kan sa, domin an samo ta ne ta hanyar karya kariyoyin da Kundin Tsarin Mulki ya tanada.
Malam El-Rufai yana kuma neman umurnin kotu da zai hana waɗanda ake ƙara amfani ko gabatar da duk wata shaida ko kayan da aka ƙwace yayin binciken da ba bisa ƙa’ida ba a kowace shari’a da ta shafe shi.
Haka kuma yana neman a mayar masa da dukkan kayan da aka samu yayin binciken, tare da neman diyya iri-iri.
A cewar takardun da aka shigar a kotu, “takardar izinin binciken tana da manyan naƙasu, ba ta fayyace kayayyakin da za a ƙwace ba, tana ɗauke da kurakuran rubutu masu muhimmanci, sharuɗɗan aiwatarwa marasa bayani, umurni masu wuce gona da iri, kuma ba ta da hujjar zargi mai tabbaci, wanda hakan ya saɓa wa Sashe na 143–148 na Dokar Gudanar da Shari’o’in Laifuka ta 2015 (ACJA), Sashe na 36 na Dokar Hana Cin Hanci da Sauran Laifuka Masu Alaƙa ta 2000 (Dokar ICPC), da kuma kariyoyin kundin tsarin mulki kan kutse ba bisa ƙa’ida ba.”
Lauyoyin Malam El-Rufai sun yi iƙirarin cewa:
• Sashe na 143 na ACJA ya tanadi cewa dole ne neman takardar izinin bincike ta kasance tare da rubutacciyar shaida da aka rantse a kanta, wadda ke bayyana hujjojin da suka sa ake zargi, amma hakan bai cika ba a wannan lamarin, kamar yadda ake gani daga rashin cikar sashen fara shari’ar;
• Sashe na 144 ya wajabta a fayyace wurin da za a bincika da kayayyakin da ake nema domin kauce wa takardun izini na gama-gari, amma takardar ta yi amfani da kalmar “abin da aka ambata a baya” ba tare da cikakken bayani ba;
• Sashe na 146 ya tanadi cewa dole ne takardar ta kasance a tsarin da doka ta amince da shi, ba tare da kurakuran da za su iya rikitarwa ba, amma takardar na cike da kurakurai a adireshi, kwanan wata da kuma sunan yankin;
• Sashe na 147 ya ba da damar a bai wa takamaiman mutane umarnin aiwatarwa, amma takardar ta yi magana da “duk” jami’ai ba tare da takamaiman nuni ba, wanda ya wuce gona da iri kuma ba shi da alhaki;
• Sashe na 148 ya ba da damar aiwatar da bincike a lokutan da suka dace, amma kalmomin da suka saɓa juna a takardar sun haifar da ruɗani, wanda ya rage bayyananniyar ƙa’ida ta shari’a.







