Wata Babbar Kotun Jihar Delta ta bayar da umarnin gaggawa da ya hana kuma ya dakatar da Sufeto Janar na ’Yan Sanda (IGP) da Rundunar ’Yan Sanda ta Nijeriya (NPF) daga ci gaba da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu a duk faɗin ƙasar nan.
Mai Shari’a Joe Egwu, a ranar Laraba yayin bayar da umarnin, ya kuma hana ’yan sanda su tsangwami ko su kama ko su tsare ko su karɓi kuɗi ba bisa ƙa’ida ba daga jama’a da direbobi bisa wannan doka.
Kotun ta ce wannan umurnin zai ci gaba da aiki har sai an saurari kuma an yanke hukunci a kan ƙarar da ke gaban ta.
Wannan sabon umurni ya biyo bayan ƙarar da wani mai suna Mista Israel Joe ya shigar a Jihar Delta, ta hannun lauyoyin sa ƙarƙashin jagorancin Kunle Edun (SAN).
Tun da farko, a ranar Litinin, Kakakin Rundunar ’Yan Sanda ta Nijeriya, Benjamin Hundeyin, ya bada sanarwar za a ci gaba da fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu da aka taɓa dakatarwa, ya ce zai fara aiki daga ranar 2 ga Janairu, 2026.
Daga cikin umurnin da kotun ta bayar akwai umurnin wucin-gadi da ya hana IGP da Rundunar ’Yan Sanda ta Nijeriya da jami’an ta “tsayawa, tsangwama, kamawa, tsarewa, karɓar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba ko kuma hana haƙƙoƙin kundin tsarin mulki na tsare mutunci, sirri, ’yancin motsi da mallakar dukiya na mai ƙara (da sauran ’yan ƙasa/direbobi), bisa hujjar aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu, har sai an saurari kuma an yanke hukunci a kan buƙatar da aka shigar a cikin ƙarar.”
Kotun ta aje ranar 24 ga Disamba, 2025 domin ci gaba da sauraron ƙarar.







