• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Kotu ta sake hana ’yan sanda aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

ALI KANO by ALI KANO
December 18, 2025
in Labarai
A A
0
Kotu ta sake hana ’yan sanda aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu
'Yan sanda da wata mota mai duhun gilashi

'Yan sanda da wata mota mai duhun gilashi

Wata Babbar Kotun Jihar Delta ta bayar da umarnin gaggawa da ya hana kuma ya dakatar da Sufeto Janar na ’Yan Sanda (IGP) da Rundunar ’Yan Sanda ta Nijeriya (NPF) daga ci gaba da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu a duk faɗin ƙasar nan.

Mai Shari’a Joe Egwu, a ranar Laraba yayin bayar da umarnin, ya kuma hana ’yan sanda su tsangwami ko su kama ko su tsare ko su karɓi kuɗi ba bisa ƙa’ida ba daga jama’a da direbobi bisa wannan doka.

Kotun ta ce wannan umurnin zai ci gaba da aiki har sai an saurari kuma an yanke hukunci a kan ƙarar da ke gaban ta.

Wannan sabon umurni ya biyo bayan ƙarar da wani mai suna Mista Israel Joe ya shigar a Jihar Delta, ta hannun lauyoyin sa ƙarƙashin jagorancin Kunle Edun (SAN).

Tun da farko, a ranar Litinin, Kakakin Rundunar ’Yan Sanda ta Nijeriya, Benjamin Hundeyin, ya bada sanarwar za a ci gaba da fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu da aka taɓa dakatarwa, ya ce zai fara aiki daga ranar 2 ga Janairu, 2026.

Daga cikin umurnin da kotun ta bayar akwai umurnin wucin-gadi da ya hana IGP da Rundunar ’Yan Sanda ta Nijeriya da jami’an ta “tsayawa, tsangwama, kamawa, tsarewa, karɓar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba ko kuma hana haƙƙoƙin kundin tsarin mulki na tsare mutunci, sirri, ’yancin motsi da mallakar dukiya na mai ƙara (da sauran ’yan ƙasa/direbobi), bisa hujjar aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu, har sai an saurari kuma an yanke hukunci a kan buƙatar da aka shigar a cikin ƙarar.”

Kotun ta aje ranar 24 ga Disamba, 2025 domin ci gaba da sauraron ƙarar.

Tags: 'yan sandaDeltagilashi mai duhukotu
Previous Post

‘Yan kabal sun sa Buhari ya riƙa kulle ɗakin sa don kada in shiga — A’isha

Next Post

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakai don farfaɗo da Maɗaba’ar Gwamnati da aka yi watsi da ita, bayan shekaru ana tafka asara

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakai don farfaɗo da Maɗaba’ar Gwamnati da aka yi watsi da ita, bayan shekaru ana tafka asara

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakai don farfaɗo da Maɗaba’ar Gwamnati da aka yi watsi da ita, bayan shekaru ana tafka asara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!