Jami’an tsaro sun miƙa Alhaji Abdullahi Bello Boɗejo, ɗan takarar kujerar Sanatan Yankin Taraba ta Tsakiya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ga Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) a Abuja.
Bello Boɗejo dai shi ne shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore.
Jami’an tsaro ne suka kama shi a daren Alhamis bayan ya isa Jalingo ta Filin Jirgin Sama na Ɗanbaba Suntai.
A cewar mataimakin sa na musamman, Malam Umar, an kama ɗan takarar na APC ne bayan wasu abokan siyasar sa sun raka shi zuwa ofishin wata hukumar tsaro.
Da yake magana ta wayar tarho da jaridar Daily Trust, Umar ya ce an riga an kai Boɗejo Abuja kuma an miƙa shi ga EFCC.
Ya ce har yanzu ba a bayyana wa iyalan sa irin laifin da ake zargin sa da aikatawa ba.
Ya yi zargin cewa kama shi ya samo asali ne daga yadda farin jinin sa yake ƙaruwa a tseren neman kujerar Sanatan Taraba ta Tsakiya.
Ya kuma zargi wasu manyan jami’an gwamnati da ’yan siyasa a jihar da kitsa kama shi.
“Yayin da nake magana da kai yanzu, ana dab da kammala tantance ’yan takarar gwamna, na Majalisar Dattawa da ta Wakilai, kuma manufar waɗanda suka kitsa kama shi ita ce su hana shi shiga aikin tantancewar,” inji Umar.







