• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

ALI KANO by ALI KANO
May 13, 2026
in Labarai
A A
0
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Alhaji Saleh Mamman

Alhaji Saleh Mamman

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a yau Laraba ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Alhaji Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75 a gidan yari.

Mai Shari’a James Omotosho ne ya yanke masa hukuncin a yau Laraba duk da yake bai halarci zaman kotun ba inda aka yi masa shari’a kan ƙarar zargin almundahanar kuɗi da zamba ta naira biliyan 33.8 da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar.

Kotun ta samu tsohon ministan da laifi a duk tuhume-tuhume 12 da EFCC  ta shigar a kan sa, inda ta ce masu gabatar da ƙara sun tabbatar da shari’ar su ba tare da wata shakka mai ma’ana ba.

Mai Shari’a Omotosho ya umurci cewa hukuncin ɗaurin zai gudana a jere, ba a lokaci guda ba, wanda ya kai jimillar shekaru 75 a gidan yari.

Alƙalin ya yanke wa Saleh Mamman hukuncin ɗaurin shekaru bakwai-bakwai a kan tuhume-tuhume na 1, 2, 3, 6, 7, 8, 9, 10, 11 da 12 ba tare da zaɓin tara ba.

Haka kuma, ya yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru uku a tuhuma ta huɗu tare da zaɓin biyan tarar naira miliyan 10, sannan shekaru biyu a tuhuma ta biyar ba tare da zaɓin tara ba.

Alƙalin ya ce rashin halartar Saleh Mamman a kotu yayin yanke hukunci da zartar da hukuncin wata dabara ce ta ganganci domin hana gudanar da adalci yadda ya kamata.

Bisa tanade-tanaden Dokar Gudanar da Shari’ar Laifuka ta 2015, kotun ta amince da hujjar lauyan EFCC, Rotimi Oyedepo (SAN), cewa za a iya ci gaba da zartar da hukunci duk da rashin halartar wanda ake tuhuma.

Shi dai Saleh Mamman, Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne ya naɗa shi Ministan Wutar Lantarki a ranar 21 ga Agusta, 2019. A ranar 1 ga Satumba, 2021 kuma Buhari ya sallame shi daga muƙamin sa, ya maye gurbin sa da Ƙaramin Ministan Ayyuka da Gidaje, Abubakar Aliyu.

Tags: EFCChukuncikotuMai Shari’a James OmotoshoSaleh Mammanɗauri
Previous Post

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

Next Post

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa
Tsaro

’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa

May 8, 2026
Next Post
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!