• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Kotu ta kama Nnamdi Kanu da laifin ta’addanci bayan ya ƙi kare kan sa

ALI KANO by ALI KANO
November 20, 2025
in Labarai
A A
0
Kotu ta kama Nnamdi Kanu da laifin ta’addanci bayan ya ƙi kare kan sa
Shugaban IPOB, Nnamdi Kanu, a kotu

Shugaban IPOB, Nnamdi Kanu, a kotu

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa shugaban ƙungiyar kafa ƙasar Biyafra, wato Indigenous People of Biafra (IPOB) da ke tsare, Nnamdi Kanu, hukunci a kan tuhuma ta biyu cikin tuhume-tuhumen ta’addanci da ake masa, tana mai cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da shari’ar su ba tare da wata shakka ba.

Laifin, wanda yake ƙarƙashin Sashe na 16 na Dokar Hana Ta’addanci ta 2013, yana ɗauke da hukuncin kisa ko ɗaurin rai-da-rai idan aka samu wanda ake tuhuma da laifi.

A cikin hukuncin sa, Mai Shari’a James Omotosho ya bayyana cewa umarnin “a zauna a gida” wanda Kanu ya bayar a faɗin yankin Kudu-maso-gabas — tare da barazanar tashin hankali da kuma aiwatar da shi ta hanyar amfani da ƙarfi — ya zama aikin ta’addanci.

Kotu ta lura da cewa wanda ake tuhumar bai da wata dama ta doka da za ta ba shi ikon taƙaita zirga-zirgar jama’ar ƙasa, tana mai jaddada cewa Shugaban Nijeriya kaɗai, ƙarƙashin Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulki, shi ne yake da ikon sanya takunkumin motsi ta hanyar amfani da ikon dokar ta-ɓaci.

“Mutanen Kudu-maso-gabas ba za a umurce su da zama a gida ba daga wani mutum da ba jami’in gwamnatin tarayya ba ko na kowace gwamnati jiha,” inji alƙalin.

Mai Shari’a Omotosho ya ambaci bayanan shaidar da PW4 ya bayar, wanda ya yi aiki a Jihar Imo, ya kuma shaida cewa umurnin tilasta zaman gida na kowace Litinin ya bar birane har da gonaki babu jama’a tsawon shekaru.

Shaidar ta kuma danganta kisan tsohon hadimin shugaban ƙasa, Ahmed Gulak, ga wasu ‘yan bindiga da ke aiwatar da umarnin, inda ta nuna cewa an harbe Gulak har lahira kusa da filin jirgin sama yayin da yake ƙoƙarin tafiya a ranar 30 ga Mayu, 2021.

Rahoton likita da aka gabatar a matsayin Shaida PWK ya tabbatar da cewa Gulak ya mutu ne sakamakon harbin bindiga da wasu ‘yan bindiga suka yi masa, waɗanda ake zaton dakarun ƙungiyar ta’addanci ta Eastern Security Network (ESN) ne, wanda kotu ta bayyana cewa suna aiki ƙarƙashin umarni da jagorancin Kanu a matsayin shugaban IPOB.

“Bayar da umurnin tilasta zaman gida ba tare da wani ikon kundin tsarin mulki ba, tare da barazana, aikin ta’addanci ne,” inji kotun.

“Kuma wanda ake tuhuma bai gabatar da wata hujja da za ta kawar da shari’ar masu gabatar da ƙara ba, don haka ana ɗaukar cewa ya amince da hujjojin da aka gabatar.”

Alƙalin ya kammala da cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da abubuwan da ke cikin tuhuma ta biyu, wadda ta zargi Kanu da iƙirarin kasancewa memba kuma shugaban IPOB, ƙungiyar da aka haramta, saɓanin Sashe na 16 na Dokar Hana Ta’addanci.

“Saboda haka, wanda ake tuhuma an yanke masa hukunci kan tuhuma ta biyu,” inji Mai Shari’a Omotosho.

Ana sa ran za a yanke hukunci nan gaba, tare da kotu tana mai cewa hukuncin da doka ta tanada a kan laifin shi ne ɗaurin rai-da-rai ko kisa.

A baya dai, kotu ta yanke wa Kanu hukunci a kan tuhuma ta farko da ake masa bayan ta tabbatar da cewa Kanu bai gabatar da wata kariya ba ko ya ba da wani bayani da zai ƙaryata hujjojin masu gabatar da ƙara.

Yayin da yake yanke hukunci, Mai Shari’a James Omotosho ya bayyana cewa shari’ar masu gabatar da ƙara ta kasance ba a ƙalubalance ta ba sakamakon ƙin da Kanu ya yi na gabatar da cikakkiyar kariya, tare da fitar da shi daga kotu a farkon ranar saboda yawan rashin ladabi da ya nuna.

“Wannan kotu, saboda haka, ta tabbatar cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da tuhuma ta farko ba tare da wata shakka mai ma’ana ba,” inji alƙalin.

“Saboda haka, wanda ake tuhumar an yanke masa hukunci kan tuhuma ta farko.”

Tun da farko a safiyar yau, sai da Mai Shari’a James Omotosho ya bada umurnin cewa za a ci gaba da shari’a — gami da yanke hukunci – ba tare da kasancewar Nnamdi Kanu a cikin kotun ba, saboda “rashin ladabi” da shugaban IPOB ɗin ya ci gaba da nunawa a cikin kotu.

Daga nan jami’an tsaro suka raka Kanu suka fitar da shi daga kotun.

Tags: hukunciIPOBkotuNnamdi Kanuta'addanci
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin jami’an tsaro don kawar da ta’addanci — Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

Gargaɗi daga CBN: A guji yin hulɗa da Zuldal Microfinance Bank, ba shi da lasisi

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
Next Post
Gargaɗi daga CBN: A guji yin hulɗa da Zuldal Microfinance Bank, ba shi da lasisi

Gargaɗi daga CBN: A guji yin hulɗa da Zuldal Microfinance Bank, ba shi da lasisi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!