Gwamnatin Tarayya ta jaddada ƙudirin ta na kare rayuka da dukiyar dukkan ‘yan Nijeriya sakamakon hare-haren da aka kai a baya-bayan nan a sassa daban-daban na ƙasar nan.
Da yake jawabi a wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Laraba, a Radio House, Abuja, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaban Ƙasa ga iyalai da al’ummomin da suka fuskanci ayyukan ta’addanci na baya-bayan nan.
Idris ya ce: “Ku sani cewa Shugaban Ƙasa Tinubu ya tura sojoji su kawar da ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga, da sauran miyagu a duk inda suke a Nijeriya. Haka kuma, an bada umurni ga jami’an tsaron mu da su gaggauta ceto ‘yan matan makarantar Kebbi da aka sace tare da haɗa su da iyalan su.”
Ministan ya bayyana kashe wani babban Janar na soja, da sace ɗalibai a Jihar Kebbi, da kuma harin da aka kai kan wani coci a Jihar Kwara a matsayin “abin tunatarwa mai raɗaɗi game da barazanar da ƙasar nan ke fuskanta,” yana mai cewa irin waɗannan ayyukan suna ƙara ƙarfafa aniyar Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen ta’addanci.
Ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya ɗage tafiye-tafiyen sa na ƙasashen waje, ciki har da taron G20 a Afrika ta Kudu, don maida hankali kan tsaron cikin gida, tare da cewa Shugaban Ƙasar ya umurci sojoji da ‘yan sanda da su tura ƙarin jami’ai zuwa Eruku da kuma dukkanin Ƙaramar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara, don tabbatar da tsaro da kuma bada amsa cikin gaggawa.
Bugu da ƙari, Idris ya bayyana cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a halin yanzu yana Birnin Kebbi bisa umarnin Shugaban Ƙasa, inda yake tattaunawa da Gwamnan Jihar Kebbi, da manyan jami’an tsaro, da sarakunan gargajiya, da kuma iyalai na ‘yan matan makarantar da aka sace.
“Shugaba Tinubu ya kuma umurci dukkan hukumomin tsaro da su bi diddigi, su kawar, tare da lalata cibiyoyin ‘yan ta’adda da na miyagu a duk faɗin ƙasar nan,” inji Idris, kuma ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa ceto ‘yan matan makarantar Kebbi da aka sace abu ne mai matuƙar muhimmanci.
Da yake jawabi kan yunƙurin da ake yi na siffanta lamarin tsaro a matsayin lamarin addini, Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya “ba ta amince da kowace irin fassara ta addini ba” dangane da matsalolin tsaro na ƙasar nan.
Ya jaddada cewa barazanar tsaro ta Nijeriya daga ta’addanci zuwa ‘yan bindiga ta shafi ‘yan ƙasa daga dukkan addinai da asali.
Ya ce: “A wannan lokaci mai muhimmanci, haɗin kan ƙasa shi ne mafi girman abin da muke da shi. Dole ne mu ƙi yaɗuwar labaran ƙarya da rarrabuwa. Maƙiyan mu ‘yan ta’adda ne kuma miyagu da ke neman hargitsa ƙasar mu.”
Ministan ya sake nanata matsayin Nijeriya a matsayin ƙasa mai addinai daban-daban inda ‘yancin yin addini yake da kariya ta tsarin mulki.
Ya yi kira ga ‘yan ƙasa da su haɗa kai da kuma goyon bayan ƙoƙarin jami’an tsaro da ke aiki tuƙuru don tabbatar da tsaron ƙasar, yana mai cewa gwamnati tana da yaƙinin cewa ayyukan tsaro da ake gudanarwa za su kai ga gaggauta ceto ‘yan matan makarantar da aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a cikin al’ummomin da abin ya shafa.







