Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron ƙarar da ake yi wa tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, zuwa ranar 23 ga Afrilu domin gurfanar da shi a gaban kotu.
Hukumar DSS ce ta shigar da tuhume-tuhume guda uku a kan sa kan zargin sa da ido da katsalandan ba bisa ƙa’ida ba a harkokin sadarwa, bayan wasu kalamai da ya yi a wata hira ta talbijin.
Tun da farko dai kotun ta sanya ranar 25 ga Fabrairu domin gurfanar da tsohon gwamnan.
Tsohon gwamnan bai halarci zaman kotun na yau Laraba ba.
Lauyan DSS, Oluwole Aladedoyin, ya sanar da kotun cewa har yanzu tsohon gwamnan yana hannun hukumar ICPC, inda ake ci gaba da binciken sa kan zargin karkatar da kuɗaɗe.
Hakan ya sa mai shari’ar ta dage shari’ar zuwa ranar 23 ga Afrilu domin gurfanar da shi.
A makon da ya gabata, Gwamnatin Tarayya, ta hannun DSS, ta shigar da tuhume-tuhume guda uku kan El-Rufa’i bisa zargin kutse a sadarwar Ribaɗu.
El-Rufa’i ya faɗa a wata hira cewa shi da wasu da bai ambaci sunayen su ba sun saurari tattaunawar wayar Ribaɗu bayan wani ɓangare na uku ya sa mata ido. Duk da amincewar sa cewa irin wannan katsalandan ɗin ya saɓa wa doka, sai ya ce irin sa ido na haramtacciyar hanya ba sabon abu ba ne, domin wai gwamnati ma tana yi.
A cewar takardar tuhuma da gidan Channels ya samu a ranar Litinin, gwamnati ta bayyana cewa El-Rufa’i ya amince cewa shi da abokan hulɗar sa sun yi wa wayar Ribaɗu kutse sun saurari maganar sa.
Tuhumar da aka shigar a Babbar Kotun Tarayya ta Nijeriya, Sashen Shari’a na Abuja, ta bayyana Gwamnatin Tarayya a matsayin mai ƙara, yayin da El-Rufa’i yake matsayin wanda ake ƙara.







