• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Sojojin Amurka sun ce an turo wasu dakarun su zuwa Nijeriya

Daga Reuters by Daga Reuters
February 3, 2026
in Tsaro, Ƙasashen Duniya
A A
0
Sojojin Amurka sun ce an turo wasu dakarun su zuwa Nijeriya
Wani sojan Nijeriya na tsaye a kan motar soji a lokacin da Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Nijeriya ya kai rangadi a Hedikwatar Rundunar Aikin Operation Lafiya Dole, a Barikin Maimalari da ke Maiduguri, Jihar Borno, ranar 7 ga Nuwamba, 2025. (Hoto daga Ahmed Kingimi / Reuters)

Wani sojan Nijeriya na tsaye a kan motar soji a lokacin da Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Nijeriya ya kai rangadi a Hedikwatar Rundunar Aikin Operation Lafiya Dole, a Barikin Maimalari da ke Maiduguri, Jihar Borno, ranar 7 ga Nuwamba, 2025. (Hoto daga Ahmed Kingimi / Reuters)

Amurka ta aike da ƙaramar tawagar sojoji zuwa Nijeriya, inji janar ɗin da ke jagorantar rundunar Amurka a Afrika a ranar Talata.

Wannan ne karo na farko da aka amince a fili da kasancewar sojojin Amurka a cikin ƙasar Nijeriya tun bayan harin sama da Amurka ta kai a ranar Kirsimeti.

Shugaba Donald Trump ne ya ba da umurnin kai hare-haren sama kan abin da ya bayyana a matsayin sansanonin ƙungiyar Islamic State a Nijeriya a watan Disamba, tare da cewa za a iya ƙara ɗaukar matakan soji daga Amurka a can.

A baya kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa Amurka tana gudanar da jiragen leƙen asiri a sararin samaniyar Nijeriya daga Ghana tun aƙalla ƙarshen watan Nuwamba.

Babban janar ɗin ya ce an aike da tawagar Amurka ne bayan ƙasashen biyu sun amince cewa akwai buƙatar ƙara ƙoƙari wajen yaƙi da barazanar ta’addanci a Yammacin Afrika.

“Wannan ya haifar da ƙarin haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen mu, ciki har da ƙaramar tawagar Amurka da ke kawo wasu ƙwarewa na musamman daga Amurka,” inji Janar Dagvin R.M. Anderson, shugaban rundunar sojin Amurka ta Afrika (AFRICOM), yayin taron manema labarai a yau Talata.

Anderson bai bayar da ƙarin bayani kan irin girma da nauyin aikin tawagar ba.

Ministan Tsaro, Christopher Musa, ya tabbatar da cewa wata tawaga tana aiki a Nijeriya, amma shi ma bai yi ƙarin bayani ba.

Wani tsohon jami’in Amurka ya ce alamar hakan na nuna tawagar Amurka na taka muhimmiyar rawa wajen tattara bayanan sirri da kuma taimaka wa sojojin Nijeriya su kai hare-hare kan ƙungiyoyin da ke da alaƙa da ta’addanci.

Nijeriya ta fuskanci matsin lamba mai tsanani daga Amurka bayan Shugaba Trump ya zargi ƙasar da ke Yammacin Afrika da gazawa wajen kare Kiristoci daga mayaƙa masu iƙirarin Musulunci da ke aiki a yankin arewa-maso-yamma.

Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin tsananta wa Kiristoci da gangan, tana cewa tana kai hari ne kan mayaƙan Musulunci da sauran ƙungiyoyin ‘yan bindiga da ke kai hare-hare ga fararen hula—Kirista da Musulmi.

Mayaƙan Boko Haram da na Islamic State West Africa Province (ISWAP) dai sun ƙara tsananta hare-hare kan ayarin motocin sojoji da fararen hula, yayin da arewa-maso-yamma ke ci gaba da zama cibiyar tashin hankalin Musulunci da ya shafe shekaru 17.

Rundunar sojin Amurka ta Afrika (AFRICOM) ta ce an kai harin a Jihar Sokoto tare da haɗin gwiwar hukumomin Nijeriya, kuma harin ya kashe mayaƙan ISIS da dama.

Harin ya biyo bayan gargaɗin da Trump ya fara bayarwa a ƙarshen Oktoba, inda ya ce Kiristanci na fuskantar “barazanar wanzuwa” a Nijeriya, tare da barazanar shiga tsakani ta soji a ƙasar kan abin da ya bayyana a matsayin gazawar dakatar da tashin hankalin da ake yi wa al’ummar Kirista.

Tags: AFRICOMISISShugabaDonaldTrumpsojinAmurkata'addanci
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin horar da ’yan Nijeriya miliyan 10 kan hadahadar kuɗi

Next Post

Cikar Neja shekara 50: Minista ya yi kira da a sabunta ƙudiri don samun makoma mai ƙarfi

Related Posts

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce
Ƙasashen Duniya

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce

April 24, 2026
Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma
Ƙasashen Duniya

Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma

April 20, 2026
Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa
Ƙasashen Duniya

Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa

April 20, 2026
Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran
Ƙasashen Duniya

Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran

April 18, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
Next Post
Cikar Neja shekara 50: Minista ya yi kira da a sabunta ƙudiri don samun makoma mai ƙarfi

Cikar Neja shekara 50: Minista ya yi kira da a sabunta ƙudiri don samun makoma mai ƙarfi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!