Rundunar Sojin Nijeriya ta Joint Task Force North East, Operation Haɗin Kai, ta bayyana cewa ta kama wani da ake zargin ɗan kunar baƙin wake ne tare da kame wasu kayayyaki da ake shirin amfani da su wajen ƙera na’urorin fashewa na hannu (IEDs) a Jihar Borno.
Jami’in yaɗa labarai na Hedikwatar Joint Task Force (Arewa Maso Gabas) Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, inda ya ce kamen ya biyo bayan ci gaba da gudanar da haɗin gwiwar ayyukan tsaro da kuma tattara sahihin bayanan sirri domin tabbatar da tsaron garin Banki a Karamar Hukumar Bama.
Ayyukan sun gudana ne ƙarƙashin jagorancin dakarun Bataliya ta 152 Task Force, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro.
Ya ce: “Da misalin ƙarfe 1740 na ranar Litinin, 29 ga Disamba, 2025, jami’an da aka tura wajen Babban Masallacin Banki sun kama wani da ake zargin ɗan ƙunar baƙin wake ne mai suna Abubakar Mustapha.
“An same shi ɗauke da sassan IEDs da aka riga aka shirya, abin da ke nuna cewa yana da niyyar kai hari nan take.”
A cewar sa, binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Bama ne, kuma an gano yana ɗauke da wasu ƙarin kayayyakin da ke da alaƙa da ayyukan ta’addanci.
“Yanzu haka ana yi masa cikakken bincike domin gano masu ɗaukar nauyin sa, abokan hulɗar sa, da kuma yiwuwar alaƙar sa da ƙungiyoyin ’yan ta’adda da ke aiki a yankin,” inji Uba.


A wani lamari irin wannan, dakarun da aka jibge a ƙofar iyakar Kamaru da Nijeriya sun tare wata mota ƙirar Fijo da ke ɗauke da buhuna shida na takin uriya, wanda wani muhimmin sinadari ne da ake yawan amfani da shi wajen ƙera makaman IED.
Uba ya ce nan take aka ƙwace motar da takin uriya ɗin tare da kai su hannun sojoji.
Ya ƙara da cewa, ci gaba da amfani da bayanan sirri da aka samu daga wannan tarewa ya kai ga kama dillalin takin, tare da ƙwato ƙarin buhuna shida na uriya, wanda ya kai adadin abin da aka ƙwato gaba ɗaya zuwa buhuna goma sha biyu.
Dukkan waɗanda ake zargi da kuma kayayyakin da aka ƙwato suna hannun hukumomi domin ci gaba da bincike da ɗaukar matakan doka da suka dace, inji shi.

Kakakin rundunar ya ce: “Dakarun JTF NE OPHK na ci gaba da mamaye yankunan da ke ƙarƙashin kulawar su ta hanyar tsattsauran sintiri, ayyukan tsaro bisa bayanan sirri, da kuma kasancewa a yankuna ba tare da yankewa ba, domin hana ’yan ta’addan JAS/ISWAP saƙat da kuma daƙile hare-hare kan fararen hula da muhimman gine-gine.
“Ƙwarin gwiwa da ingancin faɗa na dakarun mu na nan daram kuma abin gamsarwa, yayin da ake ci gaba da aiwatar da ayyuka bisa ga umarnin dawo da zaman lafiya da tsaro mai ɗorewa a faɗin Arewa-maso-gabas.
“Sojoji suna sake tabbatar wa da al’umma aniyar su ta kare rayuka da dukiyoyi ba tare da sassauci ba, tare da roƙon jama’a da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai cikin lokaci ga hukumomin tsaro domin tallafa wa ayyukan yaƙi da ta’addanci da ake gudanarwa.”







