Kotun Tarayya da ke Abuja, a yau Talata, ta bayar da umurnin tsare Mista Abubakar Malami, SAN, tsohon Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF); ɗan sa da kuma wanda ake tuhuma tare da su a Gidan Gyaran Hali na Kuje, har zuwa lokacin da za a saurari buƙatar belin su.
Mai Shari’a Emeka Nwite, a cikin hukuncin da ya yanke kan buƙatar beli ta fatar baki da lauyan su, Joseph Daudu, SAN, ya gabatar, ya ce domin adalci da sauraron shari’a cikin gaskiya, ya dace a bai wa masu gabatar da ƙara damar mayar da martani kan buƙatar belin da masu kare kai suka riga suka shigar.
Ya ce: “Na saurari bayanan lauyoyin ɓangarorin biyu, sannan na duba dokokin da suka dace.
“Ba jayayya cewa an shigar da buƙatar beli daga hannun waɗanda ake tuhuma.
“Ba jayayya cewa an miƙa buƙatar belin ga masu gabatar da ƙara.
“Haka kuma ba jayayya cewa ba za a iya janye wannan buƙata daga hannun waɗanda ake tuhuma ba,” inji shi.
Mai Shari’a Nwite ya ƙara da cewa, ko da yake kotu na da ikon bayar da beli, dole ne hakan ya biyo bayan martanin da masu gabatar da ƙara za su bayar kan buƙatar belin da aka shigar tun farko.
A cewar sa, zai zama kamar kwanton ɓauna ne idan kotu ta bayar da beli alhali masu gabatar da ƙara ba su mayar da martani ba.
Ya ce: “Wannan zai karya haƙƙin sauraron shari’a cikin adalci ga masu gabatar da ƙara.
“Na yi imanin cewa adalci zai tabbata idan aka bai wa masu gabatar da ƙara damar mayar da martani kan buƙatar belin da aka shigar.”
Mai Shari’a Nwite, wanda ya bayar da umurnin tsare waɗanda ake tuhuma a Gidan Gyaran Hali na Kuje har zuwa sauraron buƙatar belin su, ya ɗage shari’ar zuwa ranar 2 ga Janairu domin sauraro.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Hukumar EFCC, a cikin tuhumar da aka sanya wa lamba: FHC/ABJ/CR/700/2025, ta ayyana tsohon ministann, da Hajiya Bashir Asabe da Abubakar Abdul’aziz Malami a matsayin na 1, na 2 da na 3 a jerin waɗanda ake tuhuma, bi da bi, a shari’ar zargin safarar kuɗaɗe.







