• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Friday, May 15, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Kotu ta tsare Malami, matar sa da ɗan sa a Gidan Gyaran Hali na Kuje

Wakilin Mu by Wakilin Mu
December 30, 2025
in Labarai
A A
0
Kotu ta tsare Malami, matar sa da ɗan sa a Gidan Gyaran Hali na Kuje
Abubakar Malami, SAN, matar sa Hajiya Asabe Bashir, da ɗan sa Abubakar Abdul'aziz Malami (Haɗa hotuna: EFCC/X)

Abubakar Malami, SAN, matar sa Hajiya Asabe Bashir, da ɗan sa Abubakar Abdul'aziz Malami (Haɗa hotuna: EFCC/X)

Kotun Tarayya da ke Abuja, a yau Talata, ta bayar da umurnin tsare Mista Abubakar Malami, SAN, tsohon Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF); ɗan sa da kuma wanda ake tuhuma tare da su a Gidan Gyaran Hali na Kuje, har zuwa lokacin da za a saurari buƙatar belin su.

Mai Shari’a Emeka Nwite, a cikin hukuncin da ya yanke kan buƙatar beli ta fatar baki da lauyan su, Joseph Daudu, SAN, ya gabatar, ya ce domin adalci da sauraron shari’a cikin gaskiya, ya dace a bai wa masu gabatar da ƙara damar mayar da martani kan buƙatar belin da masu kare kai suka riga suka shigar.

Ya ce: “Na saurari bayanan lauyoyin ɓangarorin biyu, sannan na duba dokokin da suka dace.

“Ba jayayya cewa an shigar da buƙatar beli daga hannun waɗanda ake tuhuma.

“Ba jayayya cewa an miƙa buƙatar belin ga masu gabatar da ƙara.

“Haka kuma ba jayayya cewa ba za a iya janye wannan buƙata daga hannun waɗanda ake tuhuma ba,” inji shi.

Mai Shari’a Nwite ya ƙara da cewa, ko da yake kotu na da ikon bayar da beli, dole ne hakan ya biyo bayan martanin da masu gabatar da ƙara za su bayar kan buƙatar belin da aka shigar tun farko.

A cewar sa, zai zama kamar kwanton ɓauna ne idan kotu ta bayar da beli alhali masu gabatar da ƙara ba su mayar da martani ba.

Ya ce: “Wannan zai karya haƙƙin sauraron shari’a cikin adalci ga masu gabatar da ƙara.

“Na yi imanin cewa adalci zai tabbata idan aka bai wa masu gabatar da ƙara damar mayar da martani kan buƙatar belin da aka shigar.”

Mai Shari’a Nwite, wanda ya bayar da umurnin tsare waɗanda ake tuhuma a Gidan Gyaran Hali na Kuje har zuwa sauraron buƙatar belin su, ya ɗage shari’ar zuwa ranar 2 ga Janairu domin sauraro.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Hukumar EFCC, a cikin tuhumar da aka sanya wa lamba: FHC/ABJ/CR/700/2025, ta ayyana tsohon ministann, da Hajiya Bashir Asabe da Abubakar Abdul’aziz Malami a matsayin na 1, na 2 da na 3 a jerin waɗanda ake tuhuma, bi da bi, a shari’ar zargin safarar kuɗaɗe.

Tags: Abubakar MalamiAsabe Bashircin hanci da rashawagidan gyara haliJoseph DauduKotun TarayyaKujeMai Shari'a Emeka Nwiteshari'atuhumazargi
Previous Post

Sababbin dokokin haraji za su fara aiki ranar 1 ga Janairu kamar yadda aka tsara – Tinubu

Next Post

Sojoji sun kama wanda ake zargin ɗan ƙunar baƙin wake ne, sun tare kayayyakin haɗa bam a Borno

Related Posts

Kotu a Amurka ta ɗaure farfesa ‘yar Nijeriya watanni 70 kan satar dala miliyan 1.4
Labarai

Kotu a Amurka ta ɗaure farfesa ‘yar Nijeriya watanni 70 kan satar dala miliyan 1.4

May 14, 2026
EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Next Post
Sojoji sun kama wanda ake zargin ɗan ƙunar baƙin wake ne, sun tare kayayyakin haɗa bam a Borno

Sojoji sun kama wanda ake zargin ɗan ƙunar baƙin wake ne, sun tare kayayyakin haɗa bam a Borno

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!