Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yana gabatar da jawabin Shugaba Tinubu a Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 a birnin New York.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada buƙatar a bai wa Nijeriya kujerar dindindin a Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, a matsayin wani ɓangare na sauye-sauyen da ake son yi wa tsarin majalisar.
Tinubu, wanda mataimakin sa, Kashim Shettima, ya wakilta, ya yi wannan kira ne a lokacin da yake jawabi a zauren tattaunawa na Babban Taron majalisar karo na 80 a birnin New York.
Ya ce: “Ya zama dole Nijeriya ta samu kujerar dindindin a Kwamitin tsaro. Wannan wani muhimmin ɓangare ne na sauye-sauye domin dawo da amincewa ga wannan hukuma, wadda ita ce ginshiƙin tsarin haɗin gwiwa na duniya.”
Shugaban ya ce Majalisar Ɗinkin Duniya za ta dawo da martabar ta ne kawai idan ta dace da yanayin duniya na yanzu, ba ta bar tarihi ya ɗaure ta ba.

Ya bayyana cewa lokacin da aka kafa majalisar, Nijeriya ƙasa ce ƙarƙashin mulkin mallaka mai mutane miliyan 20, ba tare da samun wakilci a teburin da ake yanke hukunci kan makomar ta ba.
Ya ce: “Yanzu kuwa, mu ƙasa ce mai ‘yanci, muna da fiye da mutane miliyan 236, kuma an yi hasashen nan da shekaru masu zuwa za mu zama ƙasa ta uku mafi yawan jama’a a duniya.
“Nijeriya ta daɗe tana zama ginshiƙin tsaro a nahiyar Afrika, kuma abar dogaro a aikin kiyaye zaman lafiya na duniya.”
Tinubu ya bayyana cewa sojojin Nijeriya sun taka rawa a cikin ayyuka 51 daga cikin 60 na kiyaye zaman lafiya da Majalisar Ɗinkin Duniya ta gudanar tun bayan samun ‘yancin kai a 1960.
Ya da cewa ƙasar ba ta tsaya ga kan ta ba wajen yaƙar ta’addanci, inda ta yi aiki tare da maƙwabta ƙasashen Afrika ta hanyar Multinational Joint Task Force (MNJTF).
Tinubu ya ce Nijeriya ta koyi darasi daga doguwar gwagwarmaya da ta yi da ƙungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi.
Ya ce dalilin da ya sa Nijeriya take magana kan rikicin Gaza, harin da aka kai Ƙatar da sauran tashe-tashen hankali a yankin shi ne saboda ƙwarewar da ƙasar ta samu daga irin waɗannan rikice-rikice da ba sa ƙarewa inda aka fara su.
Tinubu ya ƙara da cewa Nijeriya tana goyon bayan shirin Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya na UN80 Initiative, wanda ya yi kira da a sauya tsarin hukumar domin ya dace da zamani, a kuma kawo ƙarshen maimaita ayyuka da ɓata kuɗi.







