• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Jami’an KAROTA sun kama kayan sola da kwamfutoci na naira miliyan 80 da ɓarayi suka sace a Kano

ASHAFA MURNAI BARKIYA by ASHAFA MURNAI BARKIYA
September 25, 2025
in Labarai
A A
0
Jami’an KAROTA sun kama kayan sola da kwamfutoci na naira miliyan 80 da ɓarayi suka sace a Kano
Shugaban KAROTA, Injiniya Faisal Mahmud Kabir

Shugaban KAROTA, Injiniya Faisal Mahmud Kabir

Jami’an sintiri na Hukumar Kula da Ababen Hawa wato KAROTA, sun kama kayan wuta na sola da suka haura naira miliyan 80, waɗanda da wasu ɓarayi suka sace a yankin Fagge, cikin birnin Kano.

Kakakin Yaɗa Labarai na KAROTA, Abubakar Ibrahim Sharaɗa, ya ce wasu jami’an sintiri na hukumar ce suka samu nasarar cafke ɓarayin da suka kutsa cikin ɗakin ICT na makarantar sakandare ta gwamnati, wato Aisha Shehu Government Junior Secondary School, Kuka da ke Ƙaramar Hukumar Fagge.

Da take bayani, Shugabar Makarantar Hajiya Rufa’atu Mahmud Baffa ta ce ɓarayin sun shiga ɗakin ne ta hanyar cire fale-falen rufin ɗakin da kuma farantan sola, inda suka kwashe dukkan kwamfutoci da sauran kayan aikin ICT.

Sai dai sa’a ta kuɓuce wa ɓarayin ne bayan da jami’an KAROTA suka gano kayan a lokacin sintiri, wanda hakan ya tilasta ɓarayin su ajiye kayan suka tsere da gudu.

Da yake tsokaci game da lamarin, Shugaban KAROTA, Faisal Mahmud Kabir ya ce duk da cewa jami’an sa sun bi sahun ɓarayin, ba su samu damar kama su ba, amma duk kayan da suka sace sun bar su, kuma an ƙwato su duka.

Ya kuma ya jinjina wa jami’an sa tare da ƙara masu ƙwarin gwiwa.

Kayan ICT ɗin dai an girke su ne a ƙarƙashin shirin AGILE da Bankin Duniya ke ɗaukar nauyi domin tallafa wa ƙoƙarin Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf na farfaɗo da harkar ilimi a jihar.

Shugaban KAROTA ya buƙaci gwamnatin jihar da ta ƙara tsaurara tsaro a makarantun da aka girke irin waɗannan kayayyakin domin amfanin ɗalibai.

Rahotanni sun ce ɓarayin sun ɗaure masu gadin makarantar kafin su aikata wannan ta’asa.

Shugaban KAROTA ya tabbatar da cewa an miƙa dukkan kayan da aka ƙwato ga hukumomin makarantar.

Tags: kameKAROTAkwamfutociɓarayi
Previous Post

UNGA: Nijeriya ta jaddada ‘yancin kafuwar Falasɗinu

Next Post

Nijeriya ta sake neman kujerar dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Nijeriya ta sake neman kujerar dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya

Nijeriya ta sake neman kujerar dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!