Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga ƙasashen duniya da su yafe bashi ga ƙasashe masu tasowa, yana mai cewa hakan hanya ce madaidaiciya ta wanzar da zaman lafiya da cigaba.
Tinubu, wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya wakilta, ya yi wannan kira ne a lokacin da yake gabatar da jawabin Nijeriya a Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 a birnin New York.
Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima yana gabatar da jawabin Nijeriya a Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 a birnin New York.
Ya ce: “Muna buƙatar wani sabon tsarin doka mai ɗorewa, makamancin Kotun duniya ta Kuɗi, wanda zai ba ƙasashe masu tasowa damar kuɓuta daga ɗaurewar tattalin arziki na dogaro da fitar da albarkatun kasa ba tare da sarrafawa ba.”
Tinubu ya bayyana “Lagos Action Plan” da aka tsara shekaru da dama da suka gabata, wadda ta bayyana hanyar kauce wa bashi da dogaro da shi, tare da bai wa ƙasashe damar ƙirƙira daga cikin gida a fannoni kamar noma, ma’adinai da kuma sarrafa man fetur.
Shugaban ya yaba da ƙirƙirar “African Continental Free Trade Area” (AfCFTA), yana mai cewa hakan babban abin alfahari ne da zai ƙara haɗa kan ƙasashen nahiyar.
Ya kuma ce Nijeriya ta tsaya tsayin daka wajen cimma Manufofin Cigaba masu Ɗorewa (SDGs) waɗanda, a cewar sa, za a iya cimma hakan ne ta hanyar maida hankali kan manyan manufofi na haɓakar tattalin arziki da bunƙasa arziki.

Dangane da harkokin Afrika, Tinubu ya ce Nijeriya tana maraba da yunƙurin zaman lafiya a Jamhuriyar Dimokiraɗiyyar Kwango, tare da jaddada cewa zuba jari na ƙasa da ƙasa zai iya kawo ƙarshen rikice-rikicen da suka shafi ma’adinai.
Ya ce saka hannun jari a bincike, haɓakawa da kuma sarrafa waɗannan ma’adinai a nahiyar Afrika zai taimaka wajen sauya tsarin samar da kayayyaki ga kasuwar duniya, tare da rage rikice-rikice tsakanin manyan ƙasashe.
Shugaban ya ƙara da cewa Nijeriya da sauran ƙasashen Afrika sun samu nasarori a cikin shekarun baya-bayan nan wajen gyara harkokin su na cikin gida.
“Idan aka samu sauye-sauye da za su ƙarfafa tsarin kuɗaɗen duniya, za mu iya kai wannan cigaba mataki na gaba, inda kasuwanci, zuba jari da riba za su buɗe sababbin damarmaki ga nahiyar mu,” inji shi.







