• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Ƙasashen Duniya

CBN na shirin kafa kwamitin sulhu don warware rikice-rikicen masu taurin bashi

ASHAFA MURNAI BARKIYA by ASHAFA MURNAI BARKIYA
April 17, 2026
in Ƙasashen Duniya
A A
0
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Babban Bankin Nijeriya (CBN)

Babban Bankin Nijeriya (CBN)

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya gabatar da shawarar kafa wani kwamitin sasanci wanda zai zama matakin farko wajen warware rikice-rikicen da suka shafi rance, domin rage yawan tsilla-tsilla a kotuna a harkokin bayar da lamuni da aka jingina da kadarori.

An bayyana wannan shiri ne a cikin wata sanarwa da CBN ya fitar ranar Talata, inda ya gayyaci masu ruwa da tsaki su bayar da ra’ayoyin su kan kundin dokoki da aka tsara domin kafa Kwamitin Sasanci da Warware Rikice-rikice (MDRP) a ƙarƙashin Tsarin Karɓar Lamuni ta Hanyar Jinginar Kadarori, wato STMA.

Sanarwar tana ɗauke da sa hannun Muƙaddashin Daraktan Sashen Bayar da Shawara kan Harkokin Kuɗi na CBN, P. I. Oluikpe.

“Kwamitin zai kasance, ba tare da wata kotu ko wata hukuma a Nijeriya ta shiga ba a matakin farko na sauraron duk wani rikici da ya taso daga aiwatar da dokar,” inji bankin.

CBN ya kuma ce wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin sa na ƙarfafa tsarin harkokin kuɗi da kuma inganta warware rikice-rikicen da suka shafi rance da aka jingina da kadarori masu motsi.

Ya ƙara da cewa, “CBN na ƙirƙirar ƙa’idoji da hanyoyin tafiyar da Kwamitin Sasanci da Warware Rikice-rikice.”

A cewar sanarwar, an tsara kwamitin ne domin samar da wata hanya ta musamman, mai rangwame, wacce za ta taimaka wajen warware rikice-rikicen da suka shafi ƙirƙira, cika sharuɗɗa, da kuma tilasta haƙƙin jinginar kadarori masu motsi.

Wannan shiri ya samo asali ne daga dokar ‘Secured Transactions in Movable Assets Act’ (STMA), ta 2017, wacce ta kafa kwamitin a matsayin matakin farko na sasanci da sulhu tsakanin masu bada bashi da masu karɓa.

CBN ya bayyana cewa manufar waɗannan ƙa’idoji ita ce tabbatar da tsari mai kyau, ingantacce wajen tafiyar da rikice-rikice tare da kara amincewa da tsarin bayar da lamuni da aka jingina da kadarori masu motsi.

“Babban burin waɗannan ƙa’idoji shi ne samar da tsari mai ma’ana da daidaito wajen tafiyar da rikice-rikicen STMA, tare da tabbatar da gaskiya, adalci da inganci,” inji CBN.

Ƙa’idojin sun bayyana cewa kwamitin zai yi amfani da hanyoyin warware rikice-rikice na sulhu, tare da mayar da hankali wajen kiyaye kyakkyawar alaƙa tsakanin ɓangarorin da kuma samun mafita cikin gaggawa.

Haka kuma, an ce ana sa ran kwamitin zai yanke hukunci cikin kwanaki 90 daga ranar fara sauraron kowace ƙorafi.

A ƙarƙashin tsarin da aka gabatar, dole ne ɓangarorin da ke rikici su amince da ikon kwamitin, sannan su nuna cewa sun yi ƙoƙarin warware matsalar ta hanyoyin sasanci na farko kafin kai ƙarar.

“Dole ne ɓangarorin su nuna cewa sun yi ƙoƙarin sasanta rikicin ta hanyoyi kamar tattaunawa kafin su kai batun ga kwamitin,” inji takardar.

Ƙa’idojin sun kuma ce rikice-rikicen da za a karɓa dole su kasance suna da ingantacciyar yarjejeniyar jinginar kadara, su ƙunshi sharaɗin sasanci, kuma an yi rajistar su a ‘National Collateral Registry.’

Kwamitin zai ƙunshi ƙwararru daga ɓangarorin shari’a, banki, kuɗi da kuma warware rikice-rikice, kuma kowane mamba zai kasance yana da aƙalla gogewar shekaru 10 a aikin sa.

CBN ya ce zai naɗa membobi 30, inda za a riƙa zaɓar mutane uku-uku a jere domin sauraron kowace ƙara.

Kowane rukuni zai kasance ƙarƙashin shugaba, tare da samun goyon bayan sakatariya wacce za ta kula da gudanarwa, tsara shari’o’i, jadawalin sauraro da kuma rubuce-rubuce.

Hanyoyin sasanci za su haɗa da gabatar da ƙorafi da takardu, tantancewa na farko, da kuma sauraron shari’a wanda za a iya gudanarwa a fili, ta yanar gizo, ko kuma a haɗe.

Ƙa’idojin sun kuma bayyana cewa hukuncin kwamitin zai zama dole ga ɓangarorin kuma za a iya aiwatar da shi a kotu a matsayin hukuncin da aka amince da shi.

“Hukuncin zai zama wajibi ga ɓangarorin kuma za a iya aiwatar da shi a kotu a matsayin hukuncin sulhu,” inji takardar.

Sai dai kuma, ɓangarorin suna da damar ɗaukaka ƙara bisa wasu takamaiman dalilai da suka shafi doka ko haɗe da gaskiya, cikin wani lokaci da aka ƙayyade.

Tsarin ya jaddada muhimmancin sirri, inda aka ce duk bayanan da aka tattauna a yayin sasanci dole ne a kiyaye su.

Za a samar da kuɗin gudanar da kwamitin ne daga tallafin CBN, kuɗaɗen gudanarwa da ɓangarorin da ke rikici za su biya, da kuma wasu hanyoyi.

Bankin ya ce yana neman ra’ayoyin masu ruwa da tsaki a matsayin wani ɓangare na tsarin yanke shawara na bai daya.

“A tura ra’ayoyi kafin ranar 9 ga Oktoba, 2026,” a cewar sanarwar.

Wannan mataki ya zo kusan wata guda bayan da CBN ya umarci bankuna da su taƙaita wasu ayyukan banki ga manyan masu taurin bashi, domin ƙarfafa ladabtar da masu karɓar bashi da kuma kare tsarin kuɗi.

A cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 12 ga Maris, 2026, wacce Daraktan Kula da Bankuna, Olubukola Akinwunmi ya sanya wa hannu, bankin ya umarci masu bada lamuni su ƙara tsaurara matakai kan irin waɗannan masu taurin bashi.

CBN ya ce duk masu bashi da aka sanya rancen su cikin jerin waɗanda ba sa biya a tsarin ‘Credit Risk Management System’ ko a kowanne kamfanin bayanan bashi da aka amince da shi, ba za su iya samun sabon bashi ba.

Tags: CBNPI Oluikpe
Previous Post

Ba mu buƙatar tallafin gaggawa daga IMF – Ministan Kuɗi

Next Post

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

Related Posts

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce
Ƙasashen Duniya

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce

April 24, 2026
Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma
Ƙasashen Duniya

Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma

April 20, 2026
Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa
Ƙasashen Duniya

Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa

April 20, 2026
Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran
Ƙasashen Duniya

Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran

April 18, 2026
Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta
Ƙasashen Duniya

Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta

April 3, 2026
Babban jami’in yaƙi da ta’addanci na Amurka ya yi murabus kan yaƙin Iran, ya ce Iran ba ta da wata barazana ta gaggawa
Ƙasashen Duniya

Babban jami’in yaƙi da ta’addanci na Amurka ya yi murabus kan yaƙin Iran, ya ce Iran ba ta da wata barazana ta gaggawa

March 17, 2026
Next Post
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!