Wata Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba ‘yan sanda umurnin a tsare wani lauya mai suna Ahmed Abdulrahman da wasu mutum huɗu a gidan yari saboda ana tuhumar su da yin ɓatanci a intanet da ƙage tare da ƙoƙarin zamba kan wani sanata.
Mai Shari’a Rita Ofili-Ajumogobia ce bada umurnin a yau Alhamis bayan Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda (IGP) ya gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban ta da manyan laifuffuka har 11.
Sauran waɗanda ake zargin su ne Daure David, Ishaq Abubakar Muhammed, Abdulrashid Abdullahi Musa, da Nasiru Usman Abubakar.
A cewar mai gabatar da ƙara, mutanen su biyar sun haɗu suna cin zarafin Sanatan Bauchi ta Kudu, Shehu Buba Umar, Ciyaman na Kwamitin Majalisar Dattawa kan Tsaron Ƙasa da Rahotannin Sirri.
Ana zargin su da wallafa kalaman ɓatanci, bibiya a intanet, da kuma ƙoƙarin zambatar kuɗi daga gare shi.
Waɗanda ake zargin ba su amsa laifin su ba, wanda hakan ya sa lauya mai gabatar da ƙara, Victor Okoye, ya buƙaci kotun da ta tsare su a Gidan Gyara Hali na Kuje har zuwa lokacin da za a fara sauraren ƙarar.
Sai dai lauyoyin su, bisa jagorancin Afeez Matanmi, ya buƙaci kotun da ta ba su beli, musamman wanda ake zargi na farko, Abdulrahman, wanda ya ce lauya ne da bai da niyyar gudu ko ɓata binciken da ake yi.
Ya ce da man ‘yan sanda sun riga sun ba shi beli kafin a zo kotu, kuma bai saɓa ƙa’idojin ba.
To sai dai Okoye ya ƙi yarda da wannan roƙon, ya ce waɗanda ake tuhumar ba su daina yi wa sanatan ɓatanci a intanet ba bayan an ba su belin farkon.
Ya ce: “Wanda ake zargi na farkon yana da hannu dumu-dumu a tuhuma biyar cikin sha-ɗayan da ake yi kuma ya ci gaba da wallafa ɓatanci bayan an ba shi beli. Sana’ar sa ba ta ba shi kariyar ɗaukar laifi ba.”
Ya ƙara da cewa babu dokar da ta tanadi bada damar musamman ga lauyoyi da ake zargi da aikata manyan laifuffuka.
Bayan ta gama sauraren ɓangarorin biyu, sai Mai Shari’a Ofili-Ajumogobia ta bada umurnin cewa Sashen C.I.D. da ke Area 10, Abuja, ta tsare waɗanda ake zargin har zuwa ranar 10 ga Nuwamba.
Ta umurci lauyan Abdulrahman da ya kawo sabuwar takardar amsa ga ƙin da masu ƙara suka yi na ba shi beli kafin ranar da za a koma kotu, lokacin da kotun za ta yanke hukunci kan ita takardar.
Daga nan ta ɗage sauraren shari’ar zuwa ranar 10 ga Nuwamba, 2025.
A Zargi na Ɗaya, an zargi waɗanda aka gurfanar da haɗa kai a cikin shekarar 2025 suna aikata laifin bibiyar sanatan a intanet, wanda hakan laifi ne da ya saɓa wa Sashe na 27(1)(b) na Dokar Laifukan Intanet (Cybercrimes Act) (mai gyara).
A Tuhuma ta Uku, an zargi Abdulrahman da yaɗa wani bidiyo a TikTok (“Kibanna Channel”) da YouTube inda ya yi ƙaryar cewa Sanata Umar yana da hannu wajen ɗaukar nauyin ‘yan bindiga, da nufin tada hankalin jama’a tare da jefa sanatan cikin fargabar za a kashe shi.
Sauran tuhume-tuhumen sun haɗa da ƙoƙarin ɗaya daga cikin waɗanda ake tuhumar, wato Daure David, da ƙoƙarin karɓar naira miliyan 5 daga hannun sanatan bisa burgar cewa wai zai hana wata zanga-zanga da ake so a shirya a kan sanatan.







