Gwamnatin Nijeriya ta ƙaryata iƙirarin da Shugaban Ƙasar Amurka, Donald J. Trump, ya yi cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla Nijeriya, tare da kiran da a sanya ƙasar nan cikin jerin ƙasashen da ke take ‘yancin addini.
A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar ranar Asabar mai ɗauke da sa-hannun mai magana da yawun ma’aikatar, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, gwamnatin ta ce kalaman Trump ba sa nuni ga gaskiyar halin da ake ciki a ƙasar nan.
Sanarwar ta ce: “Nijeriya tana godiya da damuwar da ƙasashe ke nunawa game da kare haƙƙin bil’adama da ‘yancin addini, amma wannan iƙirarin ba shi da tushe. ‘Yan Nijeriya mabiya dukkan addinai suna rayuwa, aiki da kuma ibada tare a cikin lumana.”

Ta ƙara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ci gaba da jajircewa wajen yaƙi da ta’addanci, ƙarfafa zumuncin addinai, da kare rayuka da haƙƙoƙin dukkan ‘yan ƙasa.
Nijeriya ta kuma bayyana cewa za ta ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Amurka domin inganta fahimtar juna kan harkokin yankin da kuma ƙoƙarin da ake yi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a ƙasar nan.







