• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Ba mu biya kuɗin fansa don a sako ɗaliban Neja ba – Gwamnatin Tarayya

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
February 24, 2026
in Tsaro
A A
0
Ba da yawu na Sa’idu Enagi ya yi rubutu kan siyasar Neja ba, kuma na dakatar da shi – Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin cewa sai da ta biya kuɗin fansa tare da sakin kwamandojin ’yan ta’adda domin a saki daliban makarantar kwana ta St. Mary’s da aka sace a Jihar Neja.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, yana mayar da martani ga wani rahoto da ke yawo a kafafen yaɗa labarai, wanda aka danganta da wasu kafafen yaɗa labarai na ƙasa da ƙasa.

Rahoton ya yi zargin cewa Gwamnatin Nijeriya ta biya gagarumin kuɗin fansa domin a sako ɗaliban.

Sai dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana zargin a matsayin “ƙarya ce tsagwaron ta kuma ba ta da tushe,” tana mai cewa hakan “na ɓata suna da ƙwarewar jami’an tsaron Nijeriya tare da raina sadaukarwar da suke yi a kullum.”

Gwamnatin ta ce duk da yake tana mutunta ’yancin ’yan jarida, “ta yi watsi da wannan labari, daga wasu majiyoyin da ba a bayyana sunayen su ba, waɗanda suke ƙoƙarin raunana amincin gwamnati mai cin gashin kan ta wadda ke aiki bisa dokokin ta.”

Ta ƙara da cewa, “Domin kawar da duk wani shakku, ba a biya ko sisin kwabo na kuɗin fansa ba, kuma ba a saki wani kwamandan ’yan ta’adda ba.”

Ministan ya ce zarge-zargen sun dogara gaba ɗaya ne kan wasu majiyoyin bayanan leƙen asiri da ba a bayyana sunayen su ba da kuma wasu da aka bayyana a matsayin “masu masaniya kan tattaunawar,” abin da ke saɓani da musantawar da hukumomin da suka dace suka yi a fili.

Ya ce Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA), da Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), da shugabannin Majalisar Dokoki duk sun fito fili sun musanta batun biyan kuɗin fansa.

Gwamnatin ta kuma ce rahoton ya ƙunshi saɓani a bayanan da ya gabatar dangane da zargin kuɗin fansa, lamarin da ya nuna zato kuma ya raunana sahihancin sa.

Game da wani zargi na musamman, ministan ya ce iƙirarin cewa an kai kuɗin fansa ta jirgi mai saukar ungulu ga ’yan tada ƙayar baya, tare da tabbatar da karɓar sa ta ƙetaren iyaka ƙarya ce.

Ya ƙara da cewa DSS ta yi watsi da wannan zargi a matsayin “ƙarya ce kuma abin dariya.”

Gwamnatin Tarayya ta jaddada cewa Nijeriya tana fuskantar wata tsararrar harkar laifi mai neman riba, tana mai cewa nasarar ceto ɗaliban ba tare da rasa rai ba ta samo asali ne daga ƙwarewar tattara bayanan sirri da kuma ingantaccen aikin rundunonin tsaro.

Ta kuma sake tabbatar da ƙudirin ta na ci gaba da tabbatar da tsaro a ƙasa, tare da kira ga kafafen yaɗa labarai da su tabbatar da sahihancin bayanai kafin wallafa rahotannin zato da ka iya ƙarfafa wa masu aikata laifi gwiwa ko raunana ƙwarin gwiwar jami’an tsaro.

Tags: fansaLabaranƘaryaMohammedIdrisStMarysta'addancitsaro
Previous Post

Tinubu na so gwamnoni su tallafa wa talakawa, su ƙarfafa marasa galihu

Next Post

Taron Kwamitin Tsare-tsaren Kuɗaɗe: CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa 26.5%

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa
Tsaro

’Yan sanda sun kama mutum takwas bisa zargin garkuwa da mutane, kuma sun ƙwato makamai a Nasarawa

May 8, 2026
Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
Next Post
Taron Kwamitin Tsare-tsaren Kuɗaɗe: CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa 26.5%

Taron Kwamitin Tsare-tsaren Kuɗaɗe: CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa 26.5%

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!