• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Nijeriya da Birtaniya sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi kan hijira, tsaron iyakoki, da bizar kasuwanci

IRO MAMMAN by IRO MAMMAN
March 20, 2026
in Labarai
A A
0
Nijeriya da Birtaniya sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi kan hijira, tsaron iyakoki, da bizar kasuwanci
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, da Sakatariyar Harkokin Cikin Gida ta Birtaniya, Shabana Mahmood, suna rattaba hannu kan yarjejeniyoyin 

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, da Sakatariyar Harkokin Cikin Gida ta Birtaniya, Shabana Mahmood, suna rattaba hannu kan yarjejeniyoyin 

Nijeriya da Birtaniya sun rattaba hannu kan manyan yarjejeniyoyi uku da suka shafi haɗin gwiwar harkokin hijira, laifuffukan shige-da-fice na tsari, tsaron iyakoki, da kuma faɗaɗa bizar kasuwanci ga kamfanonin Birtaniya da ke aiki a Nijeriya.

An bayyana yarjejeniyoyin ne a cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta fitar a shafin ta na X a jiya Alhamis, a matsayin wani ɓangare na tattaunawar da ake ci gaba da yi yayin ziyarar aiki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai Birtaniya.

An ruwaito Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, yana cewa yarjejeniyoyin “suna nuna ƙoƙarin Nijeriya na kafa tsarin hijira mai gaskiya, bisa ƙa’ida, wanda yake da tsaro, tsari mai kyau kuma mai amfani ga ɓangarorin biyu.”

Ya ƙara da cewa za su taimaka wajen magance “cin zarafin hanyoyin doka” tare da ƙarfafa tsaron iyakoki.

Ya kuma bayyana cewa ana sa ran yarjejeniyoyin za su inganta kasuwanci tare da sauƙaƙa zirga-zirgar harkokin kasuwanci, wanda hakan zai tallafa wa manyan manufofin tattalin arzikin Gwamnatin Tarayya.

A cewar sa, shirye-shiryen suna goyon bayan burin Nijeriya na kaiwa tattalin arzikin dala tiriliyan ɗaya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, ta hanyar kawar da shingayen da ke da alaƙa da hijira ba bisa ƙa’ida ba.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa an rattaba hannu kan yarjejeniyoyin tare da Sakatariyar Harkokin Cikin Gida ta Birtaniya, Shabana Mahmood, da wakiliyar kasuwancin Birtaniya, Florence Eshalomi.

Yarjejeniyoyin suna nuna wani muhimmin mataki a dangantakar Nijeriya da Birtaniya, inda suke ƙarfafa haɗin gwiwa a fannonin tafiyar da harkokin hijira, tsaro, da bunƙasar tattalin arziki.

Rattaba hannu kan yarjejeniyoyin hijira da biza tsakanin Nijeriya da Birtaniya suna zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da wasu yarjejeniyoyi da hulɗoɗi tsakanin ƙasashen biyu yayin ziyarar kwanaki biyu da Tinubu ke yi a Birtaniya.

Ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da suka fito daga ziyarar shi ne yarjejeniyar samar da kuɗaɗe fam miliyan 746 domin sabunta tashoshin jiragen ruwa na Legas.

Tashar Jiragen Ruwa ta Legas da ke Apapa da kuma tashar Tin Can Island suna da matuƙar muhimmanci ga tattalin arzikin teku na Nijeriya, domin su ne manyan ƙofofin shigo da kaya da fitar da su.

Tashoshin suna sarrafa kaso mai yawa na jigilar kaya a ƙasar nan, kuma suna da muhimmanci wajen ayyukan kwastam, samar da kuɗaɗen shiga, da kuma gaba ɗaya harkokin tattalin arziki.

Tags: BirtaniyaOlubunmi Tunji-OjoShabana Mahmoodyarjejeniyoyi
Previous Post

Rikicin ADC ya rincaɓe yayin da shugabannin ta na jihohi 36 suka maka NWC a kotu

Next Post

Mu APGA ba za mu tsaida ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027 ba, Tinubu za mu yi — Soludo

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Mu APGA ba za mu tsaida ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027 ba, Tinubu za mu yi — Soludo

Mu APGA ba za mu tsaida ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027 ba, Tinubu za mu yi — Soludo

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!