Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Ibrahim Waiya (a hagu), yana karɓar rahoton daga Shugaban kwamitin, Malam Aminu Ahmad
Kwamitin da ke kula da kafa Ƙungiyar Tsofaffin ‘Yan Jarida ta Jihar Kano (League of Veteran Journalists), ya miƙa takardar tsarin kafa ƙungiyar, wato draft charter, ga Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Abdullahi Ibrahim Waiya.
An kafa ƙungiyar ne a kan manufofi da suka haɗa da ƙarfafa ƙa’idoji da ɗabi’un aikin jarida; bayar da shawarwari da jagoranci ga sababbin ’yan jarida, haɓaka haɗin kai da fahimtar juna tsakanin tsofaffi da sababbin masu aikin jarida a jihar da kuma ƙungiyar za ta kasance mai inganci wadda za ta taimaka wajen horaswa da ɗaga matsayin sababbin ’yan jarida.
Haka kuma za ta kula da ɗabi’a da mutuncin aikin jarida da ƙara gina amincewar jama’a ga hanyoyin sadarwa da gwamnati ke amfani da su.
Membobin kwamitin sun haɗa da Farfasa Umar Faruk, Muhammad Ɗanyaro, Farfesa Maitaimako, Dakta Sule Ya’u Sule, Alhaji Abdulƙadir Ibrahim, Hauwa Sulaiman Zaharaddeen, da Mustapha Gambo Muhammad.
Dakta Aminu Umar ne sakataren kwamitin, yayin da Malam Aminu Ahmad ya jagoranci kwamitin a matsayin shugaba.







