• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni, ya maida ofishin kwamitin afuwa zuwa Ma’aikatar Shari’a

Wakilin Mu by Wakilin Mu
October 29, 2025
in Labarai
A A
0
Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni, ya maida ofishin kwamitin afuwa zuwa Ma’aikatar Shari’a
Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan takardun bada afuwa da sassauci ga wasu mutane da aka yanke wa hukunci bisa laifuffuka daban-daban, a wani mataki na aiwatar da ikon sa na yin afuwa bisa kundin tsarin mulki.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, shugaban ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar Majalisar Ƙoli ta Ƙasa da kuma bayan samun ra’ayoyin jama’a kan batun.

Sai dai bayan sake duba jerin sunayen waɗanda za su ci gajiyar afuwar, an cire waɗanda aka samu da manyan laifuffuka irin su garkuwa da mutane, safarar miyagun ƙwayoyi, cinikin mutane, zamba, da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

A cewar fadar Shugaban Ƙasa, wannan matakin ya zama dole saboda laifuffukan da suka shafi tsaro da tasirin su ga al’umma, da kuma buƙatar kare haƙƙin waɗanda aka zalunta da ƙarfafa gwiwar hukumomin tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa an tura sabuwar takardar sunayen waɗanda suka cancanci afuwa zuwa hukumar kula da gidajen gyaran hali domin aiwatar da shi.

Tinubu ya kuma bayar da umarnin mayar da ofishin sakatariyar kwamitin bada afuwa daga Ma’aikatar Ayyukan Musamman zuwa Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya.

Bugu da ƙari, ya umurci Babban Lauyan Ƙasa, da ya fitar da sababbin ƙa’idoji da za su jagoranci tsarin bada afuwa nan gaba, ciki har da shawarwari da hukumomin shari’a kafin ɗaukar mataki.

Shugaban Ƙasar ya gode wa jama’a da masu ruwa da tsaki bisa shawarwari da suka bayar, tare da tabbatar da ƙudirin gwamnatin sa na inganta tsarin shari’a da tabbatar da adalci a Nijeriya.

Tags: afuwarShugaba Bola Ahmed TinubuYafiyar Shugaban Ƙasa
Previous Post

Shettima ya yi kira ga Arewa da ta goyi bayan ayyukan Tinubu

Next Post

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
Next Post
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!