Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan takardun bada afuwa da sassauci ga wasu mutane da aka yanke wa hukunci bisa laifuffuka daban-daban, a wani mataki na aiwatar da ikon sa na yin afuwa bisa kundin tsarin mulki.
A cikin wata sanarwa da mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, shugaban ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar Majalisar Ƙoli ta Ƙasa da kuma bayan samun ra’ayoyin jama’a kan batun.
Sai dai bayan sake duba jerin sunayen waɗanda za su ci gajiyar afuwar, an cire waɗanda aka samu da manyan laifuffuka irin su garkuwa da mutane, safarar miyagun ƙwayoyi, cinikin mutane, zamba, da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba.
A cewar fadar Shugaban Ƙasa, wannan matakin ya zama dole saboda laifuffukan da suka shafi tsaro da tasirin su ga al’umma, da kuma buƙatar kare haƙƙin waɗanda aka zalunta da ƙarfafa gwiwar hukumomin tsaro.
Sanarwar ta ƙara da cewa an tura sabuwar takardar sunayen waɗanda suka cancanci afuwa zuwa hukumar kula da gidajen gyaran hali domin aiwatar da shi.
Tinubu ya kuma bayar da umarnin mayar da ofishin sakatariyar kwamitin bada afuwa daga Ma’aikatar Ayyukan Musamman zuwa Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya.
Bugu da ƙari, ya umurci Babban Lauyan Ƙasa, da ya fitar da sababbin ƙa’idoji da za su jagoranci tsarin bada afuwa nan gaba, ciki har da shawarwari da hukumomin shari’a kafin ɗaukar mataki.
Shugaban Ƙasar ya gode wa jama’a da masu ruwa da tsaki bisa shawarwari da suka bayar, tare da tabbatar da ƙudirin gwamnatin sa na inganta tsarin shari’a da tabbatar da adalci a Nijeriya.







