• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Shettima ya yi kira ga Arewa da ta goyi bayan ayyukan Tinubu

ALI KANO by ALI KANO
October 29, 2025
in Labarai
A A
0
Shettima ya yi kira ga Arewa da ta goyi bayan ayyukan Tinubu
Daga dama: Shettima yana yi wa shugabannin ACF marhabin a ofis ɗin sa

Daga dama: Shettima yana yi wa shugabannin ACF marhabin a ofis ɗin sa

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya nemi Arewa da ta yi watsi da masu neman wargaza ƙasa.

Ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar shugabannin Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (Arewa Consultative Forum, ACF) a yau.

Ƙungiyar ta kai ziyarar ne a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kwamitin Dattawan ƙungiyar, Alhaji Bashir Dalhatu.

A jawabin sa ga shugabannin na ACF, Shettima ya yi kira ga ƙungiyar da ta mara wa Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya.

Ya ce, “Babu lokacin da ya fi dacewa kamar yanzu da shugabannin Arewa za su haɗu a wuri guda wajen goyon bayan ƙoƙarin da gwamnatin Tinubu take yi domin fitar da ƙasar nan daga ƙangin matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ta daɗe tana ciki.

“Ina kira ga membobin wannan babbar ƙungiyar wannan yanki da ta ƙi amincewa da ƙulle-ƙullen waɗansu tsiraru masu neman su wargaza haɗin kan Nijeriya.

“Ina so in nuna cewa akwai bambanci tsakanin zari da rashin gamsuwa da wani al’amari, kamar yadda masu ƙirƙirar sabon rikici suke kawowa. A yayin da wasu ƙorafe-ƙorafen suna tasowa ne daga damuwar gaskiya ta neman adalci da gaskiya, wasu kuwa zari ne ke haifar da su — ta hanyar yin amfani da rikici don son rai.”

Tags: ACFBashir DalhatuKashim Shettimaziyara
Previous Post

Ba a tauye ’yancin addini a Nijeriya, inji Ministan Yaɗa Labarai a hira da CNN

Next Post

Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni, ya maida ofishin kwamitin afuwa zuwa Ma’aikatar Shari’a

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni, ya maida ofishin kwamitin afuwa zuwa Ma’aikatar Shari’a

Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni, ya maida ofishin kwamitin afuwa zuwa Ma’aikatar Shari’a

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!