Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya nemi Arewa da ta yi watsi da masu neman wargaza ƙasa.
Ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar shugabannin Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (Arewa Consultative Forum, ACF) a yau.
Ƙungiyar ta kai ziyarar ne a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kwamitin Dattawan ƙungiyar, Alhaji Bashir Dalhatu.
A jawabin sa ga shugabannin na ACF, Shettima ya yi kira ga ƙungiyar da ta mara wa Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya.
Ya ce, “Babu lokacin da ya fi dacewa kamar yanzu da shugabannin Arewa za su haɗu a wuri guda wajen goyon bayan ƙoƙarin da gwamnatin Tinubu take yi domin fitar da ƙasar nan daga ƙangin matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ta daɗe tana ciki.
“Ina kira ga membobin wannan babbar ƙungiyar wannan yanki da ta ƙi amincewa da ƙulle-ƙullen waɗansu tsiraru masu neman su wargaza haɗin kan Nijeriya.
“Ina so in nuna cewa akwai bambanci tsakanin zari da rashin gamsuwa da wani al’amari, kamar yadda masu ƙirƙirar sabon rikici suke kawowa. A yayin da wasu ƙorafe-ƙorafen suna tasowa ne daga damuwar gaskiya ta neman adalci da gaskiya, wasu kuwa zari ne ke haifar da su — ta hanyar yin amfani da rikici don son rai.”







