Sojojin “Operation Haɗin Kai” sun sake samun gagarumar nasara a yaƙin da suke yi da ’yan ta’adda a Arewa-maso-gabas, inda suka kashe wani babban kwamandan ƙungiyar ISWAP mai suna Julaibib a yankin Kimba, cikin Ƙaramar Hukumar Damboa ta Jihar Borno.
Bayanai sun nuna cewa marigayin na daga cikin manyan jagororin da ke ta’addanci a yankin Gujba na Timbuktu Triangle, kuma kashe shi ya jefa ’yan ISWAP cikin ruɗani tare da raunana tsarin jagoranci da umarnin su.
A wasu hare-hare na daban, sojojin tare da haɗin gwiwar “Civilian Joint Task Force” sun kashe ’yan ta’adda uku a wani kwanton ɓauna tsakanin Ngazalgana da Lamusheri a Borno, inda suka ƙwato bindigogin ƙirar AK-47 guda biyu.
Haka kuma, a Tsokorok da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza, sojoji sun fatattaki ’yan Boko Haram/ISWAP, suka kashe guda ɗaya tare da ƙwato babura biyu, ba tare da asara a ɓangaren sojoji ba.
A Jihar Adamawa kuwa, sojoji sun daƙile yunƙurin fashi da makami a Mubi ta Arewa, inda suka kama mutum biyu da ake zargi, sannan suka ƙwato makamai da kayayyaki.
A wani sintiri kuma, sojoji tare da ’yan sa-kai sun fafata da ’yan ta’adda a yankin Amtasa–Washim, suka ceto wata mata da aka sace tare da ƙwato bindigogi da harsasai.
Rundunar “Operation Haɗin Kai” ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da aiki tuƙuru domin tabbatar da tsaro da dawo da zaman lafiya a Arewa-maso-gabas.







