A safiyar yau Asabar a Kaduna, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya halarci ɗaurin auren Nadiya Abba Dasuƙi, ‘yar Abba Dasuƙi, Durɓin Sakkwato, da Baffa Salihi Abdullahi, wanda aka gudanar a tsohon Masallacin Juma’a na Sultan Bello.
Shettima ya tsaya a matsayin waliyyin amarya, inda ya ba da Nadiya auren ga iyalan ango.
Shi kuma Wazirin Dutse, Alhaji Bashir Mohammed Ɗalhatu, shi ne wakilin ango.
Bikin ya samu halartar ‘yan’uwa da abokan arziki, malamai da manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Daga cikin mahalarta akwai Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Mohammed Namadi Sambo; Minista, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi; Sanata Bala Ibn Na’Allah; tsohon mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan tsaron ƙasa (NSA), Sambo Dasuki; Shugaban JIBWIS na ƙasa, Sheikh Bala Lau; Sheikh Ahmad Gumi, tare da sauran manyan jami’an gwamnati, dattawa masu daraja, masu riƙe da sarautun gargajiya, ‘yan kasuwa, da malaman addini.
A wannan wuri kuma, Mataimakin Shugaban Ƙasar ya halarci wani ɗaurin auren na daban da ya shafi gidan Sanata Bala Ibn Na’Allah, inda aka ɗaura auren ɗan’uwan sa, Ishaq Sa’idu Wasagu, ɗan marigayi Sarkin Wasagu, Muhammad Tanko, da Habiba Aliyu Datsama (Ummi), ‘yar DCM Aliyu Bawa Datsama.
Shettima ya yi roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya albarkaci aurarrakin biyun, Ya ba ma’auratan zaman lafiya da fahimtar juna, kuma Ya sanya gidajen su su zama ginshiƙan kwanciyar hankali, dauwamammiyar albarka, da zaman lafiya.








