Sojojin Runduna ta 12 da ke Lokoja, Jihar Login, sun tabbatar da kashe wani fitaccen mataimakin kwamandan ’yan bindiga a jihar mai suna Babangida Kachalla.
Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Leftana Hassan Abdullahi ya fitar ta ce an samu nasarar ne a ranar 11 ga Satumba, ƙarƙashin “Operation Accord III”, tare da haɗin gwiwar rundunonin tsaro na haɗaka (OHF).
Abdullahi ya ce rundunar ta samu sahihin bayani kan motsin ’yan bindiga a dajin Ofere da yankin Ayetoro Gbede a Ƙaramar Hukumar Ijumu, inda suka shirya masu tarko.
An yi musayar wuta mai zafi, inda sojojin suka yi nasarar halaka ɗaya daga cikin manyan kwamandojin.
Sojojin sun gano kaya da dama a wajen harin, ciki har da jakar albarushi mai ɗauke da harsasai, wayoyin hannu guda 31, magunguna irin su Tramadol, kayan tsafi, na’urar auna hawan jini, da kuma kuɗi N16,000.
Haka kuma an ga jini a wajen, abin da ke nuna cewa wasu daga cikin ’yan bindigar sun tsere da raunukan harbin bindiga.
Bincike daga baya ya tabbatar da cewa Babangida Kachalla, wanda shi ne mataimakin shugaban ƙungiyar ‘yan bindiga ta Kogi, wato Kachalla Bala Shu’aibu, shi ma ya mutu daga raunukan da ya samu.
Rundunar sojojin ta tabbatar wa da jama’ar Nijeriya ƙudirin ta na kawo ƙarshen ayyukan ’yan bindiga da tabbatar da zaman lafiya.
Haka kuma ta yi kira ga al’umma da su ci gaba da bayar da ingantattun bayanai domin taimakawa a nasarar ayyukan tsaro.







