• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Shettima Ya Tafi New York Domin Wakiltar Nijeriya A Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya 

Wakilin Mu by Wakilin Mu
September 21, 2025
in Labarai
A A
0
Shettima Ya Tafi New York Domin Wakiltar Nijeriya A Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya 
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a hanyar sa ta zuwa New York

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a hanyar sa ta zuwa New York

A yau Lahadi Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bar Abuja domin wakiltar Nijeriya a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) karo na 80 da za a gudanar a birnin New York da ke Amurka, daga gobe Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28 ga watan.

Wannan na zuwa ne bisa umarnin Shugaba Bola Tinubu, kamar yadda mai taimaka masa na musamman kan yaɗa labarai, Stanley Nkwocha, ya bayyana a wata sanarwa a Abuja.

A cewar sanarwar, Shettima zai halarci taron murnar cika shekara 80 da kafa Majalisar Ɗinkin Duniya a gobe, sannan daga ranar Talata 23 zuwa Lahadi 28 zai shiga tattaunawar manyan shugabanni a zauren babban taron.

Haka kuma a ranar Laraba, 24 ga Satumba ne zai gabatar da jawabin ƙasa na Nijeriya tsakanin ƙarfe 3 zuwa 9 na dare agogon New York.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yana hawa jirgi domin tafiya New York

Bugu da ƙari, Shettima zai shiga taro na musamman kan sauyin yanayi da Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya zai jagoranta a ranar 24 ga Satumba, inda Nijeriya za ta sanar da sababbin manufofin ta bisa Yarjejeniyar Paris.

Haka kuma zai halarci taron manyan shugabanni kan samar da gidaje masu araha da shugaban Kenya zai shirya.

Bayan kammala taron majalisar, Shettima zai zarce Frankfurt a ƙasar Jamus domin ganawa da jami’an Bankin Deutche kafin ya dawo gida Nijeriya.

Tags: Kashim ShettimaNew YorkUNGA
Previous Post

“Hasken rayuwa ta”: Tinubu ya taya matar sa Oluremi murnar cika shekaru 65 da kalmomi masu daɗi

Next Post

UNGA: Nijeriya ta goyi bayan bai wa shugaban Falasɗinu damar yin jawabi ta bidiyo bayan Amurka ta hana shi biza

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
UNGA: Nijeriya ta goyi bayan bai wa shugaban Falasɗinu damar yin jawabi ta bidiyo bayan Amurka ta hana shi biza

UNGA: Nijeriya ta goyi bayan bai wa shugaban Falasɗinu damar yin jawabi ta bidiyo bayan Amurka ta hana shi biza

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!