Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya jajanta wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, bisa rasuwar mahaifiyar sa, Hajiya Umma.
Ribaɗu ya ce: “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Na yi matuƙar jimami da jin rasuwar Hajiya Umma El-Rufai, uwar iyalan El-Rufai. Ina da kyawawan tunani na lokutan da muka yi tare da ita da kuma kulawar ta irin ta uwa.
“A irin wannan lokaci, kalmomi ba sa iya bayar da cikakken ta’aziyya kan irin wannan babban rashi. Ina miƙa ta’aziyya ta har zuci ga Mallam Nasir El-Rufai da ɗaukacin iyalan sa. Allah Maɗaukakin Sarki ya gafarta mata kurakuran ta, ya ba ta hutu na har abada a Aljannar Firdausi, kuma ya ba iyalan ƙarfin jure wannan rashi.”
Shi ma Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya aika da saƙon ta’aziyya ga iyalan El-Rufai.
Ya ce: “A madadin Gwamnati da al’ummar Jihar Kaduna, ina miƙa matuƙar ta’aziyya ta ga Mai Girma, Malam Nasir El-Rufai, da ɗaukacin iyalan El-Rufai kan rasuwar mahaifiyar su abar ƙauna, Hajiya Umma El-Rufai.
“Hajiya Umma El-Rufai ba kawai uwa mai sadaukarwa kuma shugabar iyali ba ce, har ila yau mace ce mai kyakkyawan hali na musamman, mai tsantsar gaskiya, da ƙarfi cikin natsuwa.
“Ta rayu rayuwa mai cike da jinƙai, tawali’u, da hidima mai ɗorewa, tana nuna jinƙai ga marasa ƙarfi tare da girmama duk wanda ya zo gare ta. A cikin al’ummar ta, ta kasance ginshiƙi na shawarwari da sulhu, tana ƙarfafa haɗin kai tare da zama abin koyi na ƙimomin imani, haƙuri, da karamci.
“A wannan lokaci na jimami, ina tare da iyalan El-Rufai cikin alhini, ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki da ya gafarta mata kurakuran ta, ya karɓi ayyukan ta na alheri, ya kuma ba ta mafaka ta har abada a Aljannatul Firdausi.
“Allah ya sanyaya zuciyar waɗanda suka rasa ta, ya ba su juriyar jure wannan babban rashi. Amin.”







