Jakaden Nijeriya da aka naɗa zuwa ƙasar Jamus, Cif Femi Fani-Kayode, ya ce Allah ya kiyaye kada tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Mista Peter Obi, ya zama Shugaban Nijeriya.
Sai dai bai bayar da dalilin furucin sa ba yayin wata hira da ya yi da Nigeria Today News Network.
Da yake ƙarin bayani, Fani-Kayode, tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, ya shawarci tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da ya janye burin sa na tsayawa takarar shugaban ƙasa domin bai wa wasu damar yin takara.
Ya ce, “Ina girmama tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, amma ina ganin lokaci ya yi da zai ce kawai ‘a bar wasu su ci gaba da aikin’.”
Dangane da siyasar adawa a Nijeriya, Fani-Kayode ya bayyana cewa babu wani abu kamar haka domin ta rushe.
Game da jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ya bayyana ta a matsayin ƙungiyar da ke marmarin samun mulki ba tare da wata manufa ta ciyar da ƙasa gaba ba.
Ya ce, “Ba na ganin ADC a matsayin jam’iyyar adawa: ina ganin su a matsayin ƙungiyar mutane da ke da matsananciyar sha’awar mulki. Mutane ne da aka ƙi amincewa da su, mutane da ba su da wata fata ko kaɗan ta ciyar da wannan ƙasa gaba.
“Adawa ta rushe a Nijeriya. Babu adawa domin ba su ma san yadda ake zama a matsayin ‘yan adawa ba. Ta yaya za su sanya gwamnati ta yi aiki yadda ya kamata alhali suna ta rigingimu a tsakanin su, suna faɗa a tsakanin su, kuma suna barci cikin sakaci suna minshari!”
Fani-Kayode ya kuma yi la’akari da yadda All Progressives Congress (APC) ta kasance mai ƙarfi a matsayin jam’iyyar adawa da yadda har ta taɓa kayar da jam’iyyar mai mulki ta Peoples Democratic Party (PDP).







