• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Friday, May 15, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Nijeriya za ta karɓi baƙuncin gudanar da taron farko na IPI Afrika

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
October 26, 2025
in Labarai
A A
0
Nijeriya za ta karɓi baƙuncin gudanar da taron farko na IPI Afrika
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, tare da Mista Marton Gergely da Mista Raheem Adedoyin a babban taron IPI a Vienna

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, tare da Mista Marton Gergely da Mista Raheem Adedoyin a babban taron IPI a Vienna

 

Nijeriya ta amince da karɓar baƙuncin babban taron farko na ƙasashen nahiyar Afrika na Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Duniya (IPI).

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a wurin wani taro da aka gudanar a birnin Vienna na ƙasar Austriya, inda ya gana da Shugaban Kwamitin Zartarwa na IPI, Mista Marton Gergely; da Daraktan Zartarwa na IPI, Mista Scott Griffen, da kuma wakilin Nijeriya da Afrika a hukumar, wato Mista Raheem Adedoyin.

 

A cewar sa, “Nijeriya ta amince da gudanar da taron farko na ƙungiyar ta sashen nahiyar Afrika. Wani babban abin girmamawa ne a gare mu mu yi jagoranci kamar yadda muka saba.”

 

Wannan sanarwar ta biyo bayan matakin hukumar IPI na kafa ƙungiyoyin yankuna domin kula da buƙatu na musamman na kowane yanki a cikin al’ummar IPI ta duniya.

 

Ministan ya kuma tunatar da membobin yadda Nijeriya ta gudanar da babban taron duniya na IPI a Abuja a shekarar 2018 cikin nasara, inda ya ce ƙasar nan ta shirya sosai don sake gudanar da wani taron.

 

Ko da yake ba a saka ranar taron ba tukuna, Mista Griffen ya bayyana cewa ofishin IPI da ke Vienna zai tsara cikakkun bayanai tare da Mista Adedoyin da kuma Kwamitin IPI na Nijeriya.

 

Shugaban Kwamitin Zartarwar IPI, Mista Gergely, ya yaba wa Nijeriya a matsayin jagora wajen tafiyar da dimokiraɗiyya da kuma kare ’yancin ’yan jarida.

 

Haka zalika, Mista Griffen ya jinjina wa Kwamitin IPI na Nijeriya bisa jajircewar su wajen kare ’yancin manema labarai.

 

A yayin tattaunawar, Ministan ya jawo hankalin shugabannin na IPI kan buƙatar ƙarin tallafin ƙungiyar ga Makarantar Koyon Aikin Jarida ta Nijeriya (NIJ) da ke Ogba, Legas — makarantar da IPI ta kafa tun a cikin 1971 a lokacin jagorancin marigayi Alhaji Lateef Jakande.

 

Ya bayyana cewa yanzu haka tsohon Gwamnan Jihar Ogun, Aremo Olusegun Osoba, shi ne shugaban kwamitin gudanarwar makarantar.

 

Idris, wanda yana ɗaya daga cikin manyan membobin IPI, ya kasance cikin mahalarta babban taron IPI na duniya da bikin cikar ƙungiyar shekara 75 da aka gudanar a Vienna.

 

Sauran ’yan tawagar Nijeriya a taron sun haɗa da Mista Raheem Adedoyin; da Shugaban IPI Nijeriya, Musikilu Mojeed; da tsohon mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu; da Dakta Fabian Benjamin na JAMB; da Babban Sakatare ga Gwamnan Jihar Kwara, Malam Rafiu Ajakaye; da Shugaban kamfani da jaridar Patrons Media/The Culture, Mista Steve Ayorinde; da Farfesa Abigail Ogwuensi na Jami’ar Legas; da lauya kuma mai bada shawara ga IPI Nijeriya, Mista Tobi Soniyi.

Tags: IPIMohammed IdrisVienna
Previous Post

CBN ya yi farin cikin cire Nijeriya daga ƙasashen da FATF ke kaffa-kaffar hada-hadar kuɗaɗe da su

Next Post

Nnamdi Kanu ya ƙi kare kan sa a kotu, ya ce babu tuhuma a kan sa

Related Posts

Kotu a Amurka ta ɗaure farfesa ‘yar Nijeriya watanni 70 kan satar dala miliyan 1.4
Labarai

Kotu a Amurka ta ɗaure farfesa ‘yar Nijeriya watanni 70 kan satar dala miliyan 1.4

May 14, 2026
EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Next Post
Nnamdi Kanu ya ƙi kare kan sa a kotu, ya ce babu tuhuma a kan sa

Nnamdi Kanu ya ƙi kare kan sa a kotu, ya ce babu tuhuma a kan sa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!