• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Ministan Yaɗa Labarai ya taya Ɗanlami Nmodu murnar zama Shugaban Ƙungiyar Mawallafan Onlayin

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
October 13, 2025
in Labarai
A A
0
Ministan Yaɗa Labarai ya taya Ɗanlami Nmodu murnar zama Shugaban Ƙungiyar Mawallafan Onlayin
Alhaji Ɗanlami Nmodu, Shugaban GOCOP

Alhaji Ɗanlami Nmodu, Shugaban GOCOP

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya taya Alhaji Ɗanlami Nmodu murna kan zaɓen sa a matsayin Shugaban Ƙungiyar Mawallafan Jaridun Yanar Gizo (GOCOP) a zaɓen da aka gudanar a Legas.

Idris ya ce: “Malam Nmodu, mawallafin Newsdiary Online, wanda nake da alaƙa ta abota da ta aiki da shi tsawon shekaru da dama, ɗan jarida ne nagari wanda ya tabbatar da cancantar sa a aikin jarida, kuma ya dace da wannan matsayi mai daraja.”

Ministan ya kuma yaba wa tsohuwar Shugabar GOCOP, Hajiya Maureen Chigbo, mawallafiyar RealNews Online, kan jagorancin ta na mawallafan onlayin su sama da ɗari da kuma barin “gado mai cike da daraja, ƙima, gaskiya, da cigaba mai ban-sha’awa ga ƙungiyar.”

Idris ya yi kira ga sabon Shugaban na GOCOP da abokan aikin sa na gudanarwa da su bai wa haɗin kan ƙungiyar muhimmanci, inda ya jaddada muhimmancin ƙulla kyakkyawar dangantaka a ƙungiya wadda za ta dauwama tsawon lokaci.

Ya ce: “Yayin da nake taya Nmodu murna, yana da kyau in yi kira a gare shi da ya jagoranci ƙungiyar ta hanyar haɗa kai, wanda ke tabbatar da cewa dukkan membobin GOCOP sun haɗa hannu da hannu wajen ci gaba da cimma burin ƙungiyar.”

Haka kuma, ya jaddada muhimmancin lura da “mummunan tasirin labaran ƙarya, bayanan da ba daidai ba da kuma labaran ɓarna da ke barazana ga sahihancin aikin jarida.”

Saboda haka, Idris ya yi kira ga sabon shugabannin GOCOP da su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, wadda ke jagorantar wayar da kan jama’a kan ilimin kafofin yaɗa labarai a faɗin ƙasar nan.

“Na yarda da Malam Nmodu, wanda ya gina sana’ar aikin jarida bisa gaskiya, jajircewa, ƙarfin hali, da juriyar aiki, ya kuma kawo wannan irin ƙwarewa wajen haɗin gwiwa da gwamnati domin tabbatar da aminci da ilimin kafofin watsa labarai, musamman a cikin harkar kafofin watsa labarai na gidan gizo,” inji shi.

Tags: Danlami NmoduGOCOPJaridun onlayinMohammed Idristaya murna
Previous Post

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta fara yajin aiki na mako biyu

Next Post

Allah zai bi mana haƙƙi kan yafewar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, inji iyalan marigayi Bilyaminu

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Allah zai bi mana haƙƙi kan yafewar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, inji iyalan marigayi Bilyaminu

Allah zai bi mana haƙƙi kan yafewar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, inji iyalan marigayi Bilyaminu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!