Iyalan Bilyaminu Ahmed Bello, wanda matar sa Maryam Sanda ta yi wa kisan gillar a cikin 2017, sun ce ba su aminta da yafewar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Maryam ɗin ba.
A takardar bayani da ya fitar a madadin iyalan, Dakta Bello Haliru Mohammed, OFR (Ɗangaladiman Gwandu), ya bayyana matakin da Tinubu ya ɗauka a matsayin tsantsar mugunta tare da fama ciwon da ke cikin zuciyar su, tare da wargaza nasarar da suka samu a kotu a tsawon shekaru.
Dakta Bello, wanda ya taɓa zama Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, ya ce iyalan Bilyaminu sun yi shiru ne kan ibtila’in da ya faɗa masu a ranar Lahadi, 19 ga Nuwamba, 2017, wato ranar da Maryam ta kashe mijin ta, a bisa tunanin kotu za ta yi masu adalci.
Suka ce sun ji daɗin yadda Babbar Kotun Abuja ta yanke wa Maryam Sanda hukuncin kisa a ranar 27 ga Janairu, 2020, kuma Kotun Ɗaukaka Ƙara da Kotun Ƙoli suka tabbatar da shi a 2020 da 2023.
“Mun gamsu da cewa a ƙarshe an yi adalci a shari’ar, hukuncin da ya kawo ƙarshen maganar…
“Duk da yake wadda ta aikata laifin ba ta nuna wata nadama ba a duk tsawon lokacin da ake lamarin, iyalan mamacin sun haƙura bisa hukuncin da kotuna suka yanke, suka ci gaba da rayuwar su, tare da rungumar ƙaddarar da ta faɗa wa ɗan su.”
Amma iyalan suka ce yafiyar Shugaban Ƙasa, wadda ta haɗa da mutum 175 da aka yafe wa, ciki har da wasu da aka yanke wa hukuncin kisa, ta ragargaza hanyar warkewar da suke a kai kuma ta gurɓata darajar shari’a.
“A ce Wai an bar Maryam Sanda tana yawon ta ba tare da wata tsangwama ba saboda ta’asar da ta tafka, kamar ta kashe kiyashi ne, abu ne mafi ƙasƙanci da za a iya aikata wa kowane iyali saboda wani abin ƙaunar su.”
Iyalin suka ce an nuna masu bambanci a Yafiyar Shugaban Ƙasa, kuma ba komai ba ce illa siyasa ba tare da kula da ƙuncin da aka jefa su a ciki ba.
Sun zargi magoya bayan Maryam Sanda da cewa sun riƙa yaɗa maganganun ƙarya tun lokacin da aka yi kisan, ba tare da kula da rayuwar ‘ya’yan da Maryam da Bilyaminu ba, “don kawai su samu goyon bayan jama’a.”
“Maryam, kada mu manta, da farko ta ƙi amincewa da ‘ya’yan da yanzu kuma take amfani da su don neman a sake ta.”
Suka ce shari’a tana wajen Allah Maɗaukakin Sarki “wanda zai yanke hukunci kan wannan lamari a ranar Gobe Kiyama.”







