Bayan tabbatar da laifin da aka yi wa shugaban ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) da ke tsare, Nnamdi Kanu, Gwamnatin Tarayya, a yau Alhamis, ta nemi kotu da ta yanke masa hukuncin kisa.
Babban lauyan gwamnati, Adegboyega Awomolo, SAN, shi ne ya yi wannan roƙo jim kaɗan bayan kotu ta samu Kanu da laifi a kan dukkan tuhumar ta’addanci guda bakwai da aka shigar a kan sa.
Masu gabatar da ƙara sun nace cewa yekuwar Kanu ta jawo mutuwar jami’an tsaro da dama da kuma lalata muhimman gine-ginen gwamnati, suna zargin cewa IPOB da ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Eastern Security Network (ESN), wanda ya bayyana a matsayin reshen yaƙi na ƙungiyar, sun ɗauki matakan da suka nufi tayar da hankalin ƙasa.
Ya ce wajabta hukuncin da ya fi tsanani shi ne kawai zai tabbatar da adalci ga waɗanda suka rasa rayuka da dukiyoyi sakamakon ayyukan ta’addancin Kanu.
A cewar sa, duk da cewa tuhuma ta 1, 2, 4, 5 da 6 suna ɗauke da hukuncin kisa, tuhuma ta 3 tana ɗauke da hukuncin shekaru 20 a gidan gyara hali, yayin da tuhuma ta 7 ke ɗauke da hukuncin shekaru biyar.
“Mai girma ya yi la’akari da irin nauyi da kuma tsananin laifukan ta’addancin da wanda aka yanke wa hukunci ya aikata a kan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da ke zama a Kudu-maso-gabas,” inji shi.
Bugu da ƙari, ya zargi Kanu da gaza nuna nadama ko tuba dangane da laifukan, yana mai cewa halayen sa a gaban kotu suna cike da girman kai.
Haka kuma, Gwamnatin Tarayya ta roƙi kotu da ta bayar da umurnin ƙwace dukkan kayan watsa shirye-shiryen da aka kama daga hannun Kanu, tare da hana shi samun damar amfani da na’urorin zamani ko intanet duk inda za a tsare shi don ya yi zaman hukunci.
Lauyan na gwamnati ya roƙi kotun cewa don kare lafiyar Kanu, kada a mayar da shi gidan gyaran hali na Kuje a Abuja, wanda ya taɓa fuskantar fasa kurkuku a baya.
A halin da ake ciki, kafin kotu ta ɗage zaman zuwa ƙarfe 4:10 na yamma domin yanke hukunci, ta saurari roƙon ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Ikwuano/Umuahia North and South, Hon. Obinna Aguocha, wanda ya roƙi kotu da ta sassauta hukunci.
Hukuncin kotun ya kawo ƙarshen shari’ar da aka yi wa Kanu tsawon fiye da shekaru 10.







