• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
May 4, 2026
in Labarai
A A
0
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta buƙaci a ƙara haɗin gwiwa tsakanin kafafen yaɗa labarai, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki domin magance barazanar yaɗa labaran ƙarya.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja yayin bikin Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya ta shekarar 2026 da aka gudanar a hedikwatar ma’aikatar sa da ke Radio House.

Ya ce: “Wannan gwamnati ta ba da fifiko ga haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki a kafafen yaɗa labarai da kuma abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa domin inganta aikin jarida mai inganci da kuma yaƙi da yaɗa labaran ƙarya.”

Ya bayyana ’yancin ’yan jarida a matsayin muhimmin haƙƙi da kundin tsarin mulki ya tanada, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau da zai bai wa kafafen yaɗa labarai damar gudanar da aikin su cikin ’yanci, tsaro da gaskiya.

“Gwamnatin Tarayya ta amince da ’yancin ’yan jarida, kuma za ta ci gaba da samar da yanayin da zai bai wa kafafen yaɗa labarai damar yin aikin su cikin ’yanci, tsaro da gaskiya,” inji shi.

Ministan ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakai na ƙarfafa gaskiya da samun bayanai ta hanyar cigaba da hulɗa da kafafen yaɗa labarai, aiwatar da dokar ’Yancin Samun Bayanai, da kuma saka hannun jari a hanyoyin sadarwa na jama’a.

Manyan baƙi a zauren taron

Ya kuma bayyana haɗin gwiwar Nijeriya da UNESCO wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Bayanai ta Duniya (IMILI) a Abuja a matsayin wani muhimmin mataki na ƙarfafa ilimin kafafen yaɗa labarai da bayanai da kuma inganta sadarwa mai kyau a wannan zamani na dijital.

Ministan ya buƙaci ’yan jarida da su ci gaba da kiyaye ƙwarewa da ƙa’idojin aiki, yana mai jaddada cewa dole ne ’yancin aikin jarida ya tafi tare da ɗaukar nauyin da ya rataye a wuyan jama’a.

“Ainihin gwajin ’yancin ’yan jarida ba wai a cikin furucin mu yake ba, a cikin ayyukan mu yake, yadda ’yan jarida ke gudanar da aikin su cikin tsaro, yadda ake yaɗa bayanai cikin gaskiya, da kuma yadda jama’a suke amfani da su yadda ya kamata,” inji shi.

Manyan mahalarta taron

A nata jawabin maraba, Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire, ta bayyana taron a matsayin wata dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa da inganta wayar da kan jama’a.

Ta yi kira da a ƙara haɗin kai tsakanin hukumomi domin magance ƙalubalen yaɗa labaran ƙarya, musamman la’akari da yadda kafafen sadarwa na zamani suke ƙara yaɗuwa.

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyar ta ta ci gaba da aiki tare da masu ruwa da tsaki domin gina tsarin bayanai mai ƙarfi da zai tallafa wa dimokiraɗiyya, haɗin kan ƙasa da cigaba mai ɗorewa.

Taron ya samu halartar Sufeto Janar na ’Yan Sanda, wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya wakilta; da Darakta-Janar na DSS, wanda Daraktan Tsare-Tsare, M.O. Chukwuka, ya wakilta; da Babban Sakataren Hukumar Kula da Aikin Jarida ta Nijeriya, Dakta Dilli Ezughah; da kuma Shugabar Ofishin UNESCO a Abuja, wadda Shugabar Sashen Sadarwa da Bayanai, Ms Yachat Nuhu, ta wakilta.

Tags: labaran ƙaryaMohammed Idrispress freedomRanar 'Yancin 'Yan Jarida ta Duniya
Previous Post

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

Next Post

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Shugaban Ƙasa ya taya Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris Malagi murnar cika shekaru 60
Labarai

Shugaban Ƙasa ya taya Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris Malagi murnar cika shekaru 60

May 1, 2026
Next Post
Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!