Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso, da takwaran sa na Jihar Anambra, Peter Obi, sun shiga jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) a hukumance.
Obi, wanda ya kasance ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaɓen 2023, da Kwankwaso, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), sun karɓi katunan zama membobin NDC cikin farin ciki da sowa daga magoya bayan su, jim kaɗan bayan wata ganawar sirri da shugabannin jam’iyyar.
Shugabannin biyu, waɗanda suka fice daga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), sun samu tarba daga tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Seriake Dickson, wanda shi ne jagoran jam’iyyar a matakin ƙasa.
Ku yi rajista, inji Obi ga masoyan sa
Yayin da yake jawabi ga shugabannin jam’iyya, membobi da magoya baya, tsohon gwamnan na Anambra ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da kada ta kawo rikice-rikicen siyasa cikin NDC.
Haka kuma ya roƙi da a samar da sararin dimokiraɗiyya mai ’yanci, ba tare da tsoma bakin Gwamnatin Tarayya ba.
Ya ce: “Don Allah, kada a sami shari’o’i. ’Yan jam’iyya, don Allah kada ku je kotu. Abin da muke so shi ne jam’iyya. Mata da yara za su yi alfahari da wannan jam’iyya.
“Wannan jam’iyya za ta kafa gwamnati da za ta ceto Nijeriya, za ta kafa gwamnati da za ta tabbatar da cewa ’yan Nijeriya za su rayu a cikin Nijeriya ba tare da tsoro ba, ta kuma tabbatar da cewa uwa ba za ta ƙara yin kuka kan ɗan da ya tafi makaranta bai dawo ba.
“Za mu tabbatar da cewa ’yan Nijeriya ba za su ƙara kwana cikin miliyoyi ba ba tare da sanin inda abincin gobe zai fito ba.
“Ba ma son mu ɓata lokacin mu wajen shari’a da faɗa a tsakanin mu. Muna son mu mai da hankali kan matsalolin da ke shafar talakan ɗan Nijeriya.”
Obi ya roƙi ’yan Nijeriya da magoya bayan sa da su “yi duk mai yiwuwa” domin shiga jam’iyyar.
Kwankwaso ya yi kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su yi rajista da NDC cikin gaggawa.
Ya bayyana cewa ɓangaren sa ya riga ya fara yin rajista nan take.
‘Babu Rarrabuwa, Babu Shari’a’
Tun da farko, Dickson ya bayyana cewa da shugabannin biyu, “Nijeriya za ta sake zama sabuwa.”
Ya ce: “A madadin shugabannin jam’iyyar mu da kuma a madadin ɗimbin membobin jam’iyyar mu, masu kishin ƙasa daga sassa daban-daban na ƙasar nan, waɗanda a cikin watanni biyar suka fuskanci ƙalubale suka kuma shawo kan duk shakku, tare da zuba amincewar su da yardar su a mafarki da hangen nesa na wannan jam’iyya.
“A madadin su gaba ɗaya, ina gode muku, kuma ina maraba da ku duka, musamman zuwa NDC da kuma gida na mai tawali’u.”
Shugabannin jam’iyyar na ƙasa sun ce duk da cewa NDC sabuwa ce, tana shirye ta “yi abin da ya fi ƙarfin ta”.
Dickson ya ce: “Ina maraba da ku zuwa jam’iyyar siyasa mafi saurin bunƙasa a Nijeriya. Ina maraba da ku zuwa jam’iyyar siyasa mafi kwanciyar hankali a Nijeriya.
“Ina maraba da ku zuwa jam’iyyar da ba ta da rarrabuwa, jam’iyyar da ba ta da wata shari’a ko kaɗan. Haka kuma ina maraba da ku zuwa jam’iyyar da ba ta san abin da ake kira matsayin da ake ciki kafin rikici ba.”
Ya kuma bayyana Obi da Kwankwaso a matsayin masu cikakken cancanta, yana mai cewa za a bayyana cikakkun tsare-tsaren jam’iyyar a lokacin da ya dace.







