• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Babban Hafsan Sojoji ya je Borno, ya buƙaci dakaru da su ƙara jajircewa

New Citizen Hausa by New Citizen Hausa
November 20, 2025
in Labarai
A A
0
Babban Hafsan Sojoji ya je Borno, ya buƙaci dakaru da su ƙara jajircewa
Babban Hafsan Sojojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, tare da dakarun Operation Haɗin Kai lokacin da ya ziyarce su a Maiduguri 

Babban Hafsan Sojojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, tare da dakarun Operation Haɗin Kai lokacin da ya ziyarce su a Maiduguri 

Babban Hafsan Sojojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya ja kunnen dakarun Operation Haɗin Kai (OPHK) da su ci gaba da kasancewa cikin shiri, su guji sakaci, kuma su ci gaba da ɗaukar matsayi mai ƙarfi a cikin hare-haren da ake gudanarwa kan ‘yan ta’adda a yankin Arewa-maso-gabas.

Shaibu ya yi wannan jawabi ne lokacin da ya kai ziyara ta tantance ayyukan soji a Hedikwatar Rundunar Haɗin Gwiwa ta Arewa-maso-gabas (JTF NE OPHK) da ke Maiduguri.

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanal Sani Uba, ya fitar ta bayyana cewa nufin ziyarar shi ne tantance yanayin tsaro, ƙimanta yadda ake gudanar da ayyuka, ƙarfafa daidaiton dabaru, da kuma ƙara haɗin kai da masu ruwa da tsaki domin tunkarar barazanar tsaro da ke ci gaba da addabar yankin.

Yayin da yake magana da dakarun, COAS ya yaba da jarumtaka da jajircewar su wajen fuskantar ‘yan ta’adda, yana mai kira gare su da su kasance masu himma, su ci gaba da zama cikin shiri, tare da kula da duk wani motsi don hana sababbin barazanar tasowa.

Ya jaddada buƙatar ci gaba da matsa ƙaimi a fagen aiki domin hana ‘yan ta’adda damar yin abin da suke so a ko’ina cikin yankin.

Babban Hafsan Sojojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, tare da Gwamna Umara Babagana Zulum lokacin da ya ziyarce shi a Maiduguri

Shaibu ya kuma gana da manyan hafsoshin da ke cikin rundunar, inda ya jaddada muhimmancin sa ido mai ƙarfi, kyakkyawan tsare-tsare, samun sahihan bayanan leƙen asiri, da inganta yanayin gudanar da aiki domin ci gaba da samun nasarori a Operation Haɗin Kai.

Tun farko, kwamandan rundunar JTF NE OPHK, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ya yi wa COAS bayani kan ayyukan da ake gudanarwa a halin yanzu, nasarorin da aka samu, da ƙalubalen da ake fuskanta a cikin yankin.

A wani ɓangare na ziyarar, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya kai ziyarar ban-girma ga COAS.

Gwamna Zulum ya taya Shaibu murna kan naɗin sa a matsayin Babban Hafsan Sojojin Ƙasa na 25, yana mai cewa lallai ya cancanci wannan muƙami.

Ya nuna cewa Shaibu, wanda ya riƙe manyan muƙaman kwamandoji a wannan yankin, ya taka muhimmiyar rawa wajen rage matsalolin ta’addanci a yankin.

Babban Hafsan Sojojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, tare da dakarun Operation Haɗin Kai lokacin da ya ziyarce su a Maiduguri

Zulum ya bayyana ƙwarin gwiwa cewa COAS zai ci gaba da ɗorawa kan nasarorin da ake samu wajen kawar da ragowar ‘yan ta’adda domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai ɗorewa a Jihar Borno da Arewa-maso-gabas baki ɗaya.

Ya tabbatar da aniyar gwamnati da mutanen Jihar Borno wajen ci gaba da haɗin kai da Sojojin Nijeriya da sauran hukumomin tsaro domin cigaban jihar, yankin da kuma ƙasa baki ɗaya.

Yayin da yake yaba wa gagarumin cigaban da dakarun OPHK suka samu, gwamnan ya buƙace su da kada su yi ƙasa a gwiwa saboda wasu matsalolin tsaro da ke faruwa a wasu sassan jihar, sai dai su ci gaba da jajircewa da mayar da hankali.

A cikin martanin sa, COAS ya gode wa gwamnan saboda ziyarar, ya kuma yaba da haɗin kai mai ɗorewa da ke akwai tsakanin gwamnati da rundunar OPHK.

Ya tabbatar wa gwamnan da cewa Sojojin Nijeriya za su ci gaba da ƙara ƙaimi wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Borno da dukkan Arewa-maso-gabas.

Shaibu ya samu rakiyar manyan jami’an hafsoshin soji daga Hedikwatar Sojojin Ƙasa a wannan ziyarar tantance aiki.

Tags: Arewa-maso-gabasBornoFarfesa Babagana Umara ZulumgwamnaLaftanar Janar Waidi ShaibuLaftanar Kanal Sani Ubasojoji
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta nemi a yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin kisa

Next Post

An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai-da-rai

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Kotu ta kama Nnamdi Kanu da laifin ta’addanci bayan ya ƙi kare kan sa

An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai-da-rai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!