FADAR Shugaban Ƙasa ta musanta ji-ta-ji-tar da ake yaɗawa cewa wai an hana Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shiga Fadar Shugaban Ƙasa.
A wata sanarwa da mai taimaka wa Shugaban Ƙasa kan harkokin watsa labarai a ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Stanley Nkwocha, ya fitar, ya bayyana cewa labarin ƙarya ne marar tushe da nufin tada zaune tsaye da ɓata sunan gwamnati.
Ya jaddada cewa babu wani lokaci da aka hana Shettima shiga fadar, kuma rahoton da wasu shafukan yanar gizo suka wallafa ba ya da wani tushe.
Nkwocha ya bayyana lamarin a matsayin ƙoƙarin tada fitina da neman haifar da rikici tsakanin manyan shugabannin ƙasa.
Ya ce dangantakar Shugaba Bola Tinubu da Mataimakin sa tana nan daram, inda suka gina haɗin kai da mutunta juna wajen cika alƙawuran da suka ɗauka ga ‘yan Nijeriya.
Jami’in gwamnatin ya kuma buƙaci kafafen watsa labarai da su riƙa tantance gaskiyar labarai daga sahihan majiyoyi kafin wallafawa.







