Dakarun Operation Zafin Wuta da ke ƙarƙashin Rundunar Sojojin Nijeriya ta 6 da ke Jihar Taraba, ta yi nasarar damƙe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake nema ruwa a jallo.
An kama Umar Musa Geyi a ƙauyen Jandei-Kulamu, cikin Ƙaramar Hukumar Wukari, a Jihar Taraba.
Wanda ake zargin dama yana cikin jerin ‘yan ta’addar da jami’an tsaron yankin ke nema ido-rufe.
An dai haƙƙaƙe cewa yana daga cikin gaggan masu addabar yankin da hare-haren garkuwa da mutane.
Binciken farko dai ya nuna da hannun sa a sace wani Bafulatani mai suna Alhaji Jano a Jandal-Kulala, a ranar 13 ga Nuwamba, 2025. Kuma har yanzu yana hannun masu garkuwar.

An kama Geyi kamar yadda sanarwar da Mataimakin Kakakin Runduna ta 6, Laftanar Umar Muhammad ya bayyana a cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, 23 ga Nuwamba, 2025.
Ya ce an kama Geyi lokacin da aka cafke wani kiran waya da ya yi, inda yake neman a biya diyyar Naira miliyan 20 kafin su saki Alhaji Jano.







