Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) na Ƙasa, Mista Joe Ajaero, ya ce za su yi zanga-zangar ƙasa kamar yadda ƙungiyar ta shirya gudanarwa a ranar 17 ga Disamba, ba su janye ba.
Ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan wata ziyarar girmamawa da ya kai wa Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa 19 kuma Gwamnan Jihar Gombe, Inuwa Yahaya, a birnin Gombe, babban birnin jihar.
Ajaero ya ce zanga-zangar za ta nemi matakin gaggawa da ƙarfi daga gwamnati kan matsalar rashin tsaro, yana mai jaddada cewa lamarin yanzu ya shafi kowane ɗan Nijeriya, ba tare da la’akari da matsayi ko sana’a ba.
Ya ce ayyukan ’yan bindiga da laifukan tashin hankali ba su dace da al’adar Nijeriya ba, kuma dole ne a haɗa kai wajen yin Allah-wadai da su domin sauya abin da ya kira abu mai hatsari ga ƙasa.
A cewar sa, rashin tsaro na lalata tattalin arziki tare da raunana ikon Nijeriya na jawo hankalin masu zuba jari na cikin gida da na ƙasashen waje.
Ƙungiyar ta NLC ta ba da sanarwa a ranar 8 ga Disamba cewa tana shirin gudanar da zanga-zangar ƙasa baki ɗaya kan matsalar rashin tsaro a ƙasar.
Ta yi Allah-wadai da sacewa da kisan wani ma’aikacin makaranta a harin da aka kai wata makaranta a Jihar Kebbi, tare da sukar janye jami’an tsaro daga makarantar kafin faruwar harin.
NLC ta bayyana ƙaruwar hare-haren da ake kai wa makarantu a matsayin abin tayar da hankali, tare da kiran Gwamnatin Tarayya da ta tabbatar da tsaron dukkan makarantu, musamman waɗanda ke yankuna masu nisa da kuma masu rauni.
Ƙungiyar ta kuma nuna damuwa kan rikicin da ke addabar ɓangaren manyan makarantu, yajin aikin da ƙungiyar haɗin gwiwar ma’aikatan lafiya (JOHESU) ke yi, da kuma farfaɗo da Haɗin Gwiwar Ƙwadago da Ƙungiyoyin Farar Hula (LASCO).
Haka kuma, NLC ta yi tsokaci kan halin da Jam’iyyar Labour take ciki, inda ta shawarci membobin ta da su sake daidaita jam’iyyar da ƙa’idoji, aƙida da mutuncin ma’aikata.







