Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya ƙaddamar da membobin Kwamitin Asusun Bada Bashin Bunƙasa Harkokin Noma ga ƙananan manoma (ACGSF).
Da yake ƙaddamar da kwamitin a ranar Laraba a hedikwatar CBN a Abuja, Cardoso ya tabbatar da ƙudirin bankin wajen ƙara inganta harkokin noma a Nijeriya.
Ya jaddada muhimmancin aikin asusun tun daga shekarar 1977, wajen rage haɗarin da ke tattare da bayar da rancen kuɗaɗen noma.
Ya yi kira da a rungumi sabbin dabarun ƙirƙira na zamani, waɗanda suka haɗa da amfani da fasaha da kuma hanyoyin da za su haɗa mata da matasa a cikin tsarin tallafin manoma.

Ya ce wannan asusu ya ci gaba da nuna tasiri mai ƙarfi tare da kaso na biyan bashi da ya kai tsakanin kashi 90 zuwa 98 bisa 100.
Sabon kwamitin, wanda ke ƙarƙashin shugabancin Dakta Olusegun Oshin, zai ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa, sa-ido sai kuma bin-diddigi da bibiyar ayyuka a zahiri, domin ƙarfafa samar da kayayyakin noma da inganta rayuwar al’ummun karkara.
Sabon kwamitin na ACGSF da aka ƙaddamar ɗin ya ƙunshi Dakta Olusegun Oshin a matsayin Shugaba, sai membobi da suka haɗa da: Farfesa Murtala Sabo Sagagi, Dakta Nneka Onyeali-Ikpe, Injiniya Frank Satumari Kudla, Olusola Sowemimo, Adetoun Abbi-Olaniyan, sai Mista Wondi da kuma Philip Ndanusa.
Sauran waɗanda suka halarci taron ƙaddamarwar sun haɗa da Mataimakan Gwamnan Bankin, Daraktoci na Sassa da sauran ma’aikata.

Yayin ƙaddamarwar, CBN ya ce wannan gagarumin shirin Bayar da Bashin Bunƙasa Harkokin Noma, yana da tasiri sosai, shi ya sa na aka naɗa masa waɗannan membobi na Kwamitin Asusun Sa-ido kan Shirin Bada Bashi ga Manoma.
Wannan shiri dai zai fi bada fifiko ne wajen ƙarfafa ƙananan manoma, domin ƙasa wadata ƙasa da abinci.
Da yake ƙaddamar da kwamitin, Cardoso, ya ce wannan shiri yana daga cikin tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya ta sa gaba, domin ɗora harkokin noma kan turbar ciyar da ƙasa da ‘yan ƙasa gaba, bunƙasa yankunan karkara da kuma faɗaɗa hanyoyin inganta tattalin arziki.







