Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Wale Edun, ya bayyana cewa a halin yanzu Nijeriya ba ta da wani shiri na neman tallafin kuɗi daga Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF).
Edun ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin taron Ministocin Kuɗi na Afrika, wanda aka gudanar a lokacin taron shekara-shekara na IMF da Bankin Duniya a birnin Washington DC na ƙasar Amurka.
Ministan ya nanata cewa gyaran fuska da aka yi wa tsarin tattalin arzikin ƙasar nan a cikin shekara biyu da suka gabata ya fara haifar da ɗa mai ido. Ga wasu daga cikin muhimman hujjojin da ya bayar:
• Inganta Manufofi: Gyare-gyaren sun dawo da karsashi da martaba ga manufofin tattalin arzikin Nijeriya a idon duniya.
• Dogaro da Kai: Najeriya ta fi bai wa tsarin kasuwa fifiko maimakon takura wa farashin canjin kuɗi da na man fetur da ƙarfin iko.
• Juriya: Waɗannan matakai sun taimaka wa ƙasar wajen tunkarar matsalolin tattalin arziki da suka addabi sauran ƙasashen Afrika.
Duk da cewa ya ce Nijeriya tana da juriya, Ministan ya buƙaci ƙungiyoyin kuɗi na duniya da su hanzarta fitar da tallafin dala biliyan 50 da aka yi alƙawari domin tallafa wa sauran ƙasashen Afrika da ke cikin mawuyacin hali.
A cewar sa, yayin da Nijeriya ta gina katangar kariya ta hanyar sauye-sauyen cikin gida, da yawa daga cikin ƙasashen nahiyar na fuskantar barazana kuma suna buƙatar tallafin gaggawa daga waje.
A ƙarshe, ya jaddada cewa dogaro da tsarin kasuwa ya taimaka wa Nijeriya wajen samun daidaito ba tare da samun tangarɗa mai girma a harkar kasuwanci da tattalin arziki ba.







