Wani masanin tsaro, Dakta Bulama Bukarti, ya ƙaryata iƙirarin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi cewa Gwamnatin Tarayya tana biyan kuɗaɗen fansa tare da samar da kayayyaki ga ’yan bindiga da ke addabar Nijeriya.
El-Rufai ya yi wannan zargi ne a shirin “Sunday Politics” na tashar talbijin ta Channels, inda ya ɗora alhakin taɓarɓarewar tsaro a kan gwamnati.
Sai dai a martanin sa, Bukarti ya ce kalaman El-Rufai ba su da tushe, yana mai bayyana su da cewa “siyasa ce tsagwaron ta, babu gaskiya.”
Ya bayyana cewa babu wata doka ko manufa da ta bai wa gwamnati damar biyan ’yan bindiga ko kuma tallafa musu.
A cewar sa, kuɗaɗen fansa da ake yawan ji ana biya yawanci iyalan waɗanda abin ya shafa ko al’ummarsu ne ke tarawa.
Ya kuma bayyana cewa rahotanni sun nuna ’yan bindiga sun karɓi sama da Naira biliyan 2.5 a shekarar 2025 kadai, adadin da ya ce babu wata gwamnati da za ta iya ɗauka.
Masanin tsaron ya ce matsalar tsaro a Najeriya ta fi ƙarfin dabarun soja kaɗai, inda ya danganta ta da cin hanci da rashawa wanda ya kira “babban mai ba da damar ayyukan ta’addanci.”
Ya yi gargaɗin cewa ya zama dole a guji yin zarge-zargen da ba su da tushe kan shugabannin da ke kan karagar mulki, yana mai tunatar da cewa irin waɗannan maganganu an taɓa yi a kan gwamnatocin baya ma.
Yayin da yake bayani kan tsarin rundunar sojoji, Bukarti ya jaddada cewa shugaban ƙasa ne kaɗai yake da ikon bayar da umarnin ɗaukar matakin soja.
Ya ce gwamnoni, ministocin tsaro da ma mai ba da shawara kan harkokin tsaro ba su da wannan iko.
A cewar sa, tsarin umurni daga shugaban kasa yake farawa zuwa Babban Hafsan Soja, sannan daga can zuwa kwamandojin filin daga.
A ƙarshe, Bukarti ya ce magance matsalolin tsaro a Nijeriya na buƙatar dogon lokaci, hadin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro da ’yan kasa, tare da tsaurara matakan yaƙi da cin hanci da rashawa.







