Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi magana ta wayar tarho a yau da Anthony Joshua, tsohon zakaran damben boksin na ajin heavyweight ɗan Nijeriya da Birtaniya, wanda mummunan haɗari ya ritsa da shi a Jihar Ogun, inda Joshua ya jikkata kuma abokan tafiyar sa biyu suka rasu.
Wata sanarwa ga manema labarai da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar da yammacin yau ta ruwaito Tinubu yana cewa: “Na yi magana da AJ ta wayar tarho domin in isar masa da ta’aziyya ta da kai na bisa rasuwar abokan sa biyu. Na yi masa fatan alheri tare da yi masa addu’a. Ya tabbatar mini cewa yana samun kulawa mafi kyau a asibiti.
“Har ila yau, na yi magana da mahaifiyar AJ, na yi mata addu’a. Ta nuna matuƙar godiya bisa kiran da na yi mata.
“Bugu da ƙari, na yi magana da Gwamna Dapo Abiodun, wanda ke asibiti tare da su. Gwamnan ya tabbatar mini cewa zai yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da cewa AJ ya samu kulawa mafi inganci.”
Tun da farko, a wata sanarwa da ya wallafa a shafin X, Shugaba Tinubu—wanda ke ƙasashen waje a halin yanzu—ya bayyana matuƙar juyayin sa ga ɗan damben kan haɗarin da ya faru da shi a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.
Ya ce: “Ina jajanta maka kai da iyalan ka yayin da kuke ɗauke da nauyin baƙin cikin wannan mummunan lamari. A matsayin ka na ɗan wasa, a ko da yaushe ka nuna jarumta, ladabi, da ƙaunar ƙasa mara yankewa. Waɗannan halaye ne da suka sa ka zama abin alfaharin ƙasa.
“A irin waɗannan lokuta, ya kamata mu ƙarfafa juna a matsayin ’yan’uwa maza da mata masu rabon makoma ɗaya.
“Ina roƙon Allah ya ba ka ƙarfi, hikima, da rahama a wannan lokaci mai raɗaɗi. Allah ya ba ka sauƙin murmurewa cikin gaggawa, ya kuma jiƙan waɗanda suka rasu.”







