• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Tinubu ya jajanta wa zakaran damben boksin Anthony Joshua da mahaifiyar sa ta wayar tarho kan mummunan haɗarin da ya yi

IRO MAMMAN by IRO MAMMAN
December 29, 2025
in Labarai
A A
0
Tinubu ya jajanta wa zakaran damben boksin Anthony Joshua da mahaifiyar sa ta wayar tarho kan mummunan haɗarin da ya yi
Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da Anthony Joshua a Fadar Shugaban Ƙasa a watannin baya

Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da Anthony Joshua a Fadar Shugaban Ƙasa a watannin baya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi magana ta wayar tarho a yau da Anthony Joshua, tsohon zakaran damben boksin na ajin heavyweight ɗan Nijeriya da Birtaniya, wanda mummunan haɗari ya ritsa da shi a Jihar Ogun, inda Joshua ya jikkata kuma abokan tafiyar sa biyu suka rasu.

Wata sanarwa ga manema labarai da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar da yammacin yau ta ruwaito Tinubu yana cewa: “Na yi magana da AJ ta wayar tarho domin in isar masa da ta’aziyya ta da kai na bisa rasuwar abokan sa biyu. Na yi masa fatan alheri tare da yi masa addu’a. Ya tabbatar mini cewa yana samun kulawa mafi kyau a asibiti.

“Har ila yau, na yi magana da mahaifiyar AJ, na yi mata addu’a. Ta nuna matuƙar godiya bisa kiran da na yi mata.

“Bugu da ƙari, na yi magana da Gwamna Dapo Abiodun, wanda ke asibiti tare da su. Gwamnan ya tabbatar mini cewa zai yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da cewa AJ ya samu kulawa mafi inganci.”

Tun da farko, a wata sanarwa da ya wallafa a shafin X, Shugaba Tinubu—wanda ke ƙasashen waje a halin yanzu—ya bayyana matuƙar juyayin sa ga ɗan damben kan haɗarin da ya faru da shi a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.

Ya ce: “Ina jajanta maka kai da iyalan ka yayin da kuke ɗauke da nauyin baƙin cikin wannan mummunan lamari. A matsayin ka na ɗan wasa, a ko da yaushe ka nuna jarumta, ladabi, da ƙaunar ƙasa mara yankewa. Waɗannan halaye ne da suka sa ka zama abin alfaharin ƙasa.

“A irin waɗannan lokuta, ya kamata mu ƙarfafa juna a matsayin ’yan’uwa maza da mata masu rabon makoma ɗaya.

“Ina roƙon Allah ya ba ka ƙarfi, hikima, da rahama a wannan lokaci mai raɗaɗi. Allah ya ba ka sauƙin murmurewa cikin gaggawa, ya kuma jiƙan waɗanda suka rasu.”

Tags: Anthony JoshuahaɗarijajeShugaba Bola Ahmed Tinubu
Previous Post

Yadda bankin CBN ya hana ‘yan Nijeriya fuskantar ƙarancin kuɗi a ATM da bankuna yayin hutun ƙarshen shekara

Next Post

Wani abu ya fashe a asibitin Bagudo da ke Kebbi

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
Next Post
Wani abu ya fashe a asibitin Bagudo da ke Kebbi

Wani abu ya fashe a asibitin Bagudo da ke Kebbi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!