• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Tinubu ya dawo Abuja bayan kammala ziyara a Legas

Wakilin Mu by Wakilin Mu
October 6, 2025
in Labarai
A A
0
Hayaniyar siyasar 2027 ba za ta ɗauke hankalin Tinubu daga alƙibla ba – Idris
Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu

 

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dawo Abuja yau bayan shafe kwanaki 10 na ziyarar aiki a Jihar Legas.

Shugaban ya je Legas a ranar Juma’a, 26 ga Satumba, bayan halartar bikin nadin sabon Olubadan na Ibadan, Mai Martaba Oba Rashidi Adewolu Ladoja.

A yayin da yake Lagos, Shugaban Ƙasa ya gana da manyan ’yan kasuwa da masu zuba jari, ciki har da shugaban kamfanin Global Infrastructure Partners, Bayo Ogunlesi, da tsohon shugaban UBA da Etisalat, Akeem Belo-Osagie, wanda yanzu ke shugabantar Metis Capital Partners.

Shugaba Tinubu ya kuma karɓi baƙuncin Sakatare-Janar na Hukumar Kula da Harkokin Ruwa ta Duniya (IMO), Mista Arsenio Dominguez, tare da Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Ruwa, Adegboyega Oyetola, da shugabannin hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar.

A yayin tattaunawar, Shugaban Ƙasa ya sake jaddada ƙudirin gwamnatin sa na inganta harkokin ruwa a matsayin hanyar dena dogaro da man fetur.

A daren bikin cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai, Shugaban Ƙasa ya ziyarci Jihar Imo, inda ya ƙaddamar da wasu ayyukan da Gwamna Hope Uzodimma ya aiwatar.

Haka kuma ya halarci taron kaddamar da littafin da Gwamnan ya rubuta kan tarihin shekaru 10 na mulkin jam’iyyar APC a Nijeriya.

A ranar bikin ’yancin kai, Shugaban Ƙasa ya gabatar da jawabin ƙasa kai tsaye daga fadar gwamnati ta Dodan Barracks.

Daga bisani kuma, ya ƙaddamar da sabunta Gidan wasa na ƙasa (National Theatre), wanda yanzu aka sake masa suna zuwa Cibiyar Al’adu da Fasaha ta Wole Soyinka (Wole Soyinka Centre for Culture and the Creative Arts), inda ya yi kira ga ’yan ƙasa da su riƙa yin fata mai kyau game da Nijeriya.

A ranar Asabar, 4 ga Oktoba, Shugaban Ƙasa ya ziyarci garin Jos, Jihar Filato, domin halartar jana’izar mahaifiyar Farfesa Nantawe Yilwatda, Shugaban APC na ƙasa.

A wajen jana’izar, Shugaba Tinubu ya yaba da rayuwa da jajircewar marigayiya Mama Lydia Yilwatda, tare da tabbatar wa al’ummomin Kiristoci na Arewa cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da tabbatar da adalci da daidaito tsakanin mabiya mabambantan addinai a faɗin ƙasar nam.

Previous Post

Gwamnatin Tinubu na ci gaba da tallafa wa manoman Arewa da kayan aikin gona 

Next Post

Tinubu ya bada umarnin a rage kuɗin kujerar aikin Hajji na 2026

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Tinubu ya bada umarnin a rage kuɗin kujerar aikin Hajji na 2026

Tinubu ya bada umarnin a rage kuɗin kujerar aikin Hajji na 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!