• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Tinubu ya bayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro tare da ba da umurni ga hukumomin tsaro da su ɗauki ƙarin ma’aikata

Wakilin Mu by Wakilin Mu
November 26, 2025
in Labarai
A A
0
Tinubu ya rattaba hannu a dokar kafa cibiyoyin horas da ‘yan sanda
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana dokar ta-ɓaci kan harkokin tsaro a faɗin ƙasar nan, tare da bayar da umurnin ɗaukar ƙarin jami’an tsaro da zummar ƙarfafa yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.

A cikin wata sanarwa daga fadar shugaban kasa da aka fitar ranar Laraba, Shugaba Tinubu ya ce wannan mataki ya zama dole ne sakamakon yadda sabbin hare-hare ke ci gaba da faruwa a wasu jihohin arewacin kasar.

Shugaban ya ce rundunar ‘yan sanda za ta dauki karin ’yan sanda 20,000, lamarin da zai kara yawan wadanda za su shiga aiki zuwa 50,000 gaba daya. Ya kara da cewa an ba hukumar ‘yan sanda izinin amfani da sansanonin masu bautar ƙasa (NYSC) a matsayin cibiyoyin horaswa na wucin gadi.

Shugaban ya kuma bayar da umarnin cewa jami’an da aka cire daga aikin tsaron fitattun mutane su sake samun horaswa ta musamman kafin a tura su yankunan da ke fama da matsalar tsaro.

A bangaren hukumar DSS kuwa, shugaban kasar ya ba da izinin tura duka rundunonin forest guards da aka horar domin fatattakar ’yan ta’adda da ’yan bindiga da ke boye a dazukan kasar, tare da umarnin daukar karin ma’aikata domin kara mamaye wuraren da ake zargin masu aikata laifuka na fakewa.

Shugaba Tinubu ya ce wannan mataki yana nuni da cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yanayi da zai bata tsaron kasa ba, tare da jadadda cewa “ba za a sake samun wani wurin boyewa ga miyagu ba.”

Shugaban ya jinjinawa jami’an tsaro kan ceto dalibai 24 da aka sace a jihar Kebbi da kuma mambobin coci 38 da aka kubutar a jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da kokarin ceto sauran wadanda ake tsare da su a jihar Neja da wasu sassa na kasar.

Ya kuma bukaci hafsoshin soji su ci gaba da nuna jajircewa da bin ka’idojin aiki, yana mai cewa babu wani sassauci da za a yi wajen hukunta masana aikata laifi ko wadanda ba su cika ka’ida ba.

A cikin jawabin nasa, shugaban ya bukaci Majalisar Dokoki ta kasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da suke bukata damar kafa rundunar ’yan sanda ta jiha.

Ya kuma gargadi jihohi da su yi taka-tsantsan wajen bude makarantu a yankunan da ba su da isasshen tsaro, tare da shawartar masallatai da majami’u a yankunan da ke da matsalar tsaro da su nemi kariyar jami’an tsaro kafin gudanar da ibada.

Tinubu ya jaddada cewa gwamnati ta kafa Ma’aikatar kiwon dabbobi ne domin magance rikicin manoma da makiyaya, yana mai kiran kungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo a ruga maimakon yawo da dabbobi a fili, tare da mika duk wasu makamai da ba su da lasisi.

Shugaban ya jajanta wa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a hare-haren da suka faru kwanan nan a jihohin Kebbi, Borno, Zamfara, Neja, Yobe da Kwara, tare da tunawa da jami’an soji da suka rasa rayukansu, ciki har da Janar Musa Uba.

Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su kwantar da hankali, su kasance cikin shiri, tare da ba da hadin kai wajen bayar da bayanai ga jami’an tsaro.

“Wannan lokaci ne da ya bukaci mu hadu guri daya domin kare kasa. Kada mu fada cikin fargaba. Tare za mu iya, tare za mu ci nasara,” in ji shugaban.

Tags: dokar ta-ɓaciShugaba Bola Ahmed Tinubutsaro
Previous Post

Tinubu ya naɗa sabbin jakadu zuwa Amurka, Birtaniya da Faransa

Next Post

Sojoji sun yi juyin mulki a Gini-Bissau, sun kama shugaban ƙasa

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
Next Post
Sojoji sun yi juyin mulki a Gini-Bissau, sun kama shugaban ƙasa

Sojoji sun yi juyin mulki a Gini-Bissau, sun kama shugaban ƙasa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!