Ƙasar Somaliya da Ƙungiyar Tarayyar Afrika (AU) sun yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin ƙasa mai cin gashin kan ta.
Somaliland dai ta ayyana ficewar ta daga Somaliya tun a shekarar 1991,
A cikin 1991 ne dai Jamhuriyar Somaliland, wadda ta ayyana kan ta da kan ta a arewa-maso-yammacin Somaliya, ta bayyana samun ‘yancin ta daga sauran sassan ƙasar.
A 1998 kuma wani yanki a arewa-maso-gabas, mai suna Puntland, ya ayyana kan sa a matsayin yanki mai cin gashin kan sa (“autonomous”).
Somaliland a tsawon shekaru tana neman amincewar ƙasashen duniya, inda shugaban ƙasar, Abdirahman Mohamed Abdullahi, ya sanya hakan a matsayin babban abin da ya fi ba shi muhimmanci tun bayan hawan sa mulki a bara.
A jiya Juma’a ne Shugaban Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bada sanarwar cewa ƙasar sa tana kallon Somaliland a matsayin “ƙasa mai cin gashin kan ta kuma mai cikakken iko”, lamarin da ya sa Somaliya ta bayyana wannan mataki a matsayin “harin da aka shirya kai-tsaye” kan ikon ƙasar ta, wanda zai iya lalata zaman lafiya a yankin.
Ƙungiyar Tarayyar Afrika ma ta ce wannan mataki ne na kafa wani “mummunan misali mai haɗari, wanda ke da manyan tasiri ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin nahiyar.”







