Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yi murabus daga muƙamin sa.
Mai taimaka masa kan fasaha, Ahmed Mu’azu, ya tabbatar wa jaridar The Guardian murabus ɗin a safiyar yau Talata, inda ya ce aje aikin ya fara aiki ne tun daga jiya Litinin. Ba a bayar da wani dalili a hukumance ba kan matakin.
Usman, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa a shekarar 2024, ya jagoranci aikin Hajji na farko a ƙarƙashin sa a shekarar 2025, wanda ya zama karon farko da ya kula da harkokin aikin Hajjin Nijeriya a matakin ƙasa.
An naɗa shi ne domin maye gurbin Jalal Arabi, wanda aka cire daga muƙamin yayin da ake binciken sa kan zargin karkatar da kuɗaɗen da aka fitar domin Hajjin 2024.
Sai dai, ɗan gajeren zaman sa a muƙamin ya fuskanci rikice-rikice na cikin gida da kuma zarge-zargen da suka shafi tafiyar da kuɗi da gudanarwa a lokacin aikin Hajjin 2025. Waɗannan matsaloli sun haddasa tashin hankali a cikin hukumar tare da jawo hankalin jama’a.
Rikicin ya kai ƙololuwa ne a watan jiya, lokacin da wasu kwamishinonin NAHCON suka miƙa takarda ga Shugaba Tinubu, inda suka kaɗa ƙuri’ar rashin amincewa da shugabancin Farfesan.
A cikin takardar da suka rubuta ranar 19 ga Janairu, kwamishinonin sun zarge shi da rashin bin ƙa’idojin tafiyar da kuɗi, rashin gaskiya, karya dokokin saye da sayarwa na gwamnati, da kuma aikata wasu abubuwa da suka saɓa da dokokin kuɗin hukumar.
Sun kuma yi zargin cewa an bayar da wasu kwangiloli ba tare da samun takardar “No Objection Certificate” daga Hukumar Kula da Saye da Sayarwa ta Gwamnati (BPP) ba, sannan an kashe wasu kuɗaɗe ba tare da amincewar kwamitin gudanarwa ba.
Takardar ta kuma ambaci rahotannin da ke cewa ana binciken shugaban ne daga Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC).
A cewar kwamishinonin, wannan hali ya haifar da rashin jituwa a cikin NAHCON tare da barazana ga shirye-shiryen Hajjin 2026.
Rikicin ya ja hankalin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya kira taro da manyan masu ruwa da tsaki domin sasanta ɓangarorin da ke rikici tare da dawo da zaman lafiya a cikin hukumar.
Rahotannin baya sun kuma nuna zargin kurakurai na gudanarwa a Hajjin 2025, ciki har da cewa dubban gadon da aka biya a Mina, Saudiyya, sun kasance ba a yi amfani da su ba, inda ake zargin ba a mayar da kuɗaɗen da ya kamata cikin wa’adin da aka tanada ba.
Shugaban dai ya ƙaryata zarge-zargen, yana mai cewa sun samo asali ne daga rikicin cikin gida.
Murabus ɗin Usman ya ƙara jefa jagorancin NAHCON cikin rashin tabbas a wani lokaci mai muhimmanci, yayin da shirye-shiryen Hajjin 2026 ke ƙara ɗaukar zafi.







